Labarai
Za a bada tallafin kayan Miliyan 250 ga wadanda rikici ya shafa a Jos

Asusun tallafawa wadanda wata masifa ta Shafa ya bada gudummuwar kayaking da kudin su ya kai naira miliyan 250 ga al’unmar kananan hukunomin da jihar Plateau da suka hada da Riyom, Bassa da barikin Ladi.
Gwamnan jihar Plateau Caleb Mutfwang ya fada wajen kaddamar da bada tallafin cewa, zasuyi dukkanin abin da zasu iya don tabbatar tsaron lafiya da dukiyar al’umma.
Asusun Wanda ke karkashin jagorancin Theophilus Danjuma na masu zaman kansu ne da ke mayarda hankali wajen bada tallafin ilimi, tsaftar muhalli da ruwansha da dai sauransu.
Manufar ita ce dai karfafa al’ummomin kananan hukumomin Bassa Riyom da Barikin Ladi da wannan masifar ta Shafa.
Kayayyakin da aka bada tallafi sun hada da kayayyakin abinci da na karatu.
Gwamnan Jihar Plateau yace wata manufar su ita ce mayarda al’ummomin da aka raba da gidajen su na iyaye da kakanni don su ci gaba da noma, saboda gwamnati ba tada nufin ajiye su a sansanonin ‘yan gudun hijira.
Gwamnan ya Kuma godewa wadanda suka bada wannan tallafi tare da bayyana cewa ya bada umurnin ga sakataren Gwamnatin jihar da ya kafa wani kwamiti mai zaman kansa da zai bibiyi dukkanin abubuwan da za ayi don tabbatar da gaskiya da adalci wajen rabon kaya.
Jami’ar ayukka ta Asusun Mrs. TOYOSI Akenrele Ogunsiyi ta bayyana cewa suna sane da duk wani kalubale da ake fuskanta, sai dai ba za ta iya Kamala aikin Nan.
Shugabar asusun wacce ta bayyana al’ummar jihar Plateau a matsayin masu hazaka tace zasu talafawa dukkanin masu kasuwanci domin bunkasa harkokin su.
Mrs. Akenrele Ogunsiyi tace zasu mayarda hankali wajen ganin cewa sunyi aiki da duk Wanda ya rike aikinsa da gaskiya tare da hukunta wadanda suka kasa yin aikin da aka sa su
Shi Kuma shugaban hukunar bada agajin gaggawa na jihar Mr. Sunday Abudu ya bada tabbacin cewa za ayi adalci wajen rabon kayan tallafin.
Josiah Buzum/Shafii Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
