Connect with us

Labarai

Za a bada tallafin kayan Miliyan 250 ga wadanda rikici ya shafa a Jos

Published

on

Asusun tallafawa wadanda wata masifa ta Shafa ya bada gudummuwar kayaking da kudin su ya kai naira miliyan 250 ga al’unmar kananan hukunomin da jihar Plateau da suka hada da Riyom, Bassa da barikin Ladi.

Gwamnan jihar Plateau Caleb Mutfwang ya fada wajen kaddamar da bada tallafin cewa, zasuyi dukkanin abin da zasu iya don tabbatar tsaron lafiya da dukiyar al’umma.

Asusun Wanda ke karkashin jagorancin Theophilus Danjuma na masu zaman kansu ne da ke mayarda hankali wajen bada tallafin ilimi, tsaftar muhalli da ruwansha da dai sauransu.

Manufar ita ce dai karfafa al’ummomin kananan hukumomin Bassa Riyom da Barikin Ladi da wannan masifar ta Shafa.

Kayayyakin da aka bada tallafi sun hada da kayayyakin abinci da na karatu.

Gwamnan Jihar Plateau yace wata manufar su ita ce mayarda al’ummomin da aka raba da gidajen su na iyaye da kakanni don su ci gaba da noma, saboda gwamnati ba tada nufin ajiye su a sansanonin ‘yan gudun hijira.

Gwamnan ya Kuma godewa wadanda suka bada wannan tallafi tare da bayyana cewa ya bada umurnin ga sakataren Gwamnatin jihar da ya kafa wani kwamiti mai zaman kansa da zai bibiyi dukkanin abubuwan da za ayi don tabbatar da gaskiya da adalci wajen rabon kaya.

Jami’ar ayukka ta Asusun Mrs. TOYOSI Akenrele Ogunsiyi ta bayyana cewa suna sane da duk wani kalubale da ake fuskanta, sai dai ba za ta iya Kamala aikin Nan.

Shugabar asusun wacce ta bayyana al’ummar jihar Plateau a matsayin masu hazaka tace zasu talafawa dukkanin masu kasuwanci domin bunkasa harkokin su.

Mrs. Akenrele Ogunsiyi tace zasu mayarda hankali wajen ganin cewa sunyi aiki da duk Wanda ya rike aikinsa da gaskiya tare da hukunta wadanda suka kasa yin aikin da aka sa su

Shi Kuma shugaban hukunar bada agajin gaggawa na jihar Mr. Sunday Abudu ya bada tabbacin cewa za ayi adalci wajen rabon kayan tallafin.

Josiah Buzum/Shafii Wababe

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara