Connect with us

Kasuwanci

Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Jawabi a Abu Dhabi

Published

on

Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar wa da duniya a Hadaddiyar Daular Larabawa cewa Najeriya a shirye take ta hada kai da sauran kasashe domin gina kasa mai juriya, daidaito da kuma dorewa.

 

Shugaba Tinubu ya ba da wannan tabbacin ne a rana ta biyu na makon nemo hanyoyin Dorewar makamashi maras illa da ake gudanarwa Abu Dhabi na 2025 akan “Daga Mahimmancin yanayi zuwa Ci gaban Tattalin Arziki.

 

Shugaban ya bayyana cewa, babu wata kasa guda da za ta iya tafiya a kan hanyar dorewar ita kadai, yana mai jaddada cewa, cudanya da juna a duniya na bukatar daukar matakai na bai daya, da kuma goyon bayan juna.

 

“Yakin da ake yi da sauyin yanayi ba wai wata bukata ce kawai ta muhalli ba, amma wata dama ce ta tattalin arzikin duniya don sake fasalin yanayin nahiyarmu da yanayin makamashin duniya.

 

“A matsayinmu na shugabanni, masu ruwa da tsaki da kuma ‘yan kasa na wannan duniyar tamu, mun tsaya a wani muhimmin lokaci a tarihin dan Adam. Don samun nasara, dole ne mu kirkiro sabbin abubuwa, hada kai da kuma yin aiki mai tsauri a matsayin al’ummar duniya daya,” in ji shi.

 

Da yake nanata kudurin gwamnatinsa na rage hayakin Carbon, Shugaba Tinubu ya tabbatar wa mahalarta taron cewa, gwamnatin Najeriya ta samar da shirye-shirye masu dacewa daidai da abin da ake tsammani a duniya, tare da la’akari da hasashen tattalin arziki da siyasar Najeriya.

 

Shugaba Tinubu ya yabawa shugaban kasar Hadaddiyar Daular Larabawa, Sheikh Mohamed bin Zayed bin Sultan Al Nahyan, bisa gayyatar da yayi da kuma hangen nesa wajen shirya taron.

 

Taron ya tattaro shugabannin duniya tare don yin musayar ra’ayi da ra’ayoyi kan yadda za a magance kalubalen duniya na zamaninmu tare.

 

Abdullahi Bello/Wababe

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara