Connect with us

Labarai

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

Published

on

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu a gaban Allah.

Kwamishinan Ilimi da Bunƙasa Jarin Dan Adam na jihar Kwara, Dr. Lawal Olohungbebe, ne ya bayyana hakan a wajen bikin buda baki na shekara-shekara na Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar Kwara na 2026 da aka gudanar a Ilorin.

Taron wanda ke dauke da taken “Shugabanci, Kafafen Yada Labarai da Yaki da Rashin Tsaro a Al’umma”, ya mayar da hankali kan rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen inganta zaman lafiya.

Dr. Olohungbebe ya jaddada cewa ya zama wajibi ‘yan jarida, musamman Musulmi, su rika tabbatar da gaskiya da tantance bayanai kafin wallafa su, musamman a daidai lokacin da kasar ke fuskantar kalubalen tsaro.

Ya ce addinin Musulunci ya jaddada muhimmancin tabbatar da sahihancin labari kafin yada shi, yana mai bayanin cewa Alkur’ani ya umarci muminai su binciki gaskiyar duk wani bayani kafin yada shi domin kauce wa yaudarar jama’a.

Kwamishinan ya kara da cewa jita-jita da bayanan karya ba sabon abu ba ne, domin sun kasance tun a zamanin Annabi Muhammad (SAW) lokacin da hanyoyin sadarwa suka takaita ga magana kai tsaye ko kuma wasiku.

Ya kuma gargadi ‘yan jarida da su yi la’akari da illar da wasu rahotanni ka iya haifarwa ga zaman lafiya da tsaron al’umma, tare da jaddada cewa malamai ma suna da rawar da za su taka wajen tabbatar da zaman lafiya a cikin al’umma.

A nata jawabin, Kwamishinar Raya Al’umma ta jihar Kwara, Dr. Maryam Imam, ta yaba wa kungiyar NUJ ta jihar bisa shirya wannan taro.

Ta ce taron ya bai wa mambobin kungiyar damar samun karin karfafa imaninsu a watan Ramadan, tare da karfafa musu gwiwa su ci gaba da riko da kwarewa da kyawawan dabi’u a aikinsu.

Shi ma a jawabinsa, Shugaban NUJ na jihar Kwara, Malam Lanre Ahmed, ya ce yayin da aikin sojoji shi ne kare iyakokin kasa, su kuma ‘yan jarida na da alhakin tabbatar da rahotanninsu ba su ba masu aikata tashin hankali wata dama ko karin daukaka.

Ya kuma nuna damuwa kan abin da ya kira gasa marar amfani tsakanin wasu malaman addini wajen neman daukaka, yana mai cewa ya kamata shugabannin addini su kasance abin koyi ga al’umma.

Malam Ahmed ya shawarci kafafen yada labarai da su guji yada irin wadannan sabani, maimakon haka su mayar da hankali kan batutuwan da ke karfafa hadin kai da kyawawan dabi’u.

A nasa bangaren, Shugaban Kwamitin Lafiya da Gina Jiki na Majalisar Dokokin Jihar Kwara, Seun Ogunniyi, ya bukaci ‘yan jarida su yi nazari kan darasin da bakon malamin taron ya gabatar.

Ya ce ya zama wajibi ‘yan jarida su rika tacewa da tantance labarai kafin yada su, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen inganta aikin jarida mai nagarta.

A karshe, Shugabar Kwamitin Shirya Iftar na NUJ na 2026 a jihar Kwara, Binta Abubakar Mora, ta gode wa bakon malamin bisa gabatar da muhimmin darasi da ya ba mahalarta jagoranci na ruhaniya a lokacin da kasar ke fuskantar matsalolin tsaro.

Ta ce darasin ya kuma haskaka muhimmiyar rawar da ‘yan jarida za su taka wajen taimakawa wajen magance matsalar rashin tsaro a kasa.

ALI MUHAMMAD RABIU

Labarai

Labarai14 hours ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai18 hours ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai22 hours ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai23 hours ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai1 day ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai1 day ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai1 day ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai1 day ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai4 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai4 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara