Connect with us

Labarai

Kisan ‘Yan Arewa 16 A Jihar Edo: Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Nemi Adalci

Published

on

 

 

Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta yi ala wadai da kisan gilla da aka yi wa ‘yan Arewa 16 a Uromi, Jihar Edo, a ranar 28 ga Maris, 2025.

 

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu daga Fatakwal zuwa Kano lokacin da aka kai musu farmaki, aka sare su, sannan aka banka musu wuta a abin da gidauniyar ta bayyana a matsayin abin “aikin rashin imani” na tashin hankali bisa la’akari da bambancin kabilanci.

 

A cikin wata sanarwa da Darakta-Janar na gidauniyar, Injiniya Dakta Abubakar Gambo Umar, ya fitar, gidauniyar ta nuna damuwarta kan yadda hare-haren da ake kai wa ‘yan Arewa ke ƙaruwa a wasu sassan Kudancin kasan nan, tana gargaɗin cewa irin waɗannan munanan ayyukan na barazana ga hadin kan kasa da zaman lafiya.

 

“Muna matuƙar ƙin wannan aika-aika da aka yi wa ‘yan Najeriya bisa la’akari da kabilanci da yankuna,” in ji sanarwar.

 

“Abin baƙin ciki ne cewa ‘yan ƙasa ba za su iya yin tafiye-tafiye cikin kasarsu ba cikin tsaro da kwanciyar hankali, ba tare da fargabar farmaki ko cutarwa ba.”

 

Gidauniyar ta tuna da wasu hare-haren da aka kai a baya kan ‘yan Arewa a Kudancin kasan nan.

 

“Ba zamu manta da kisan ‘yan Arewa uku a Jihar Anambra a ranar 18 ga Janairu, 2022 ba, da kisan direbobin tirela biyu a Jihar Enugu a ranar 14 ga Yuli, 2023, inda aka kona motocinsu, da kuma kisan ‘yan Arewa biyar a Jihar Delta a ranar 30 ga Oktoba, 2024,” sanarwar ta karanta.

 

“Kuma ba za mu manta da kisan gillar da aka yi wa wata mace mai ciki, Harira Jibril, da ‘ya’yanta mata guda huɗu a Jihar Ebonyi a ranar 23 ga watan Mayun 2021 ba.”

 

“Waɗannan abubuwa da makamantansu sun nuna wani yanayi mai tayar da hankali da bai kamata a yi shiru a kansa ba,” in ji gidauniyar.

 

Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Memorial ta buƙaci a gaggauta kama tare da gurfanar da masu hannu a kisan Uromi, tare da biyan diyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa.

 

“Muna buƙatar adalci cikin gaggawa, dole ne hukumomi su hukunta waɗanda suka aikata wannan ta’asa,” sanarwar ta ci gaba.

 

Haka kuma, gidauniyar ta roƙi shugabannin Kudancin kasan nan su ɗauki matakan wayar da kan al’ummominsu don gujewa ɗora laifi bisa la’akari da kabilanci da aikata ayyukan tashin hankali.

 

“Ba kowa ne ke da ikon ɗaukar doka a hannunsa ba,” in ji ta.

 

“Allah wadai kadai ba ya isa; dole ne a yi adalci.”

 

Sanarwar ta jaddada cewa kowanne ɗan Najeriya na da ‘yancin rayuwa da aiki a kowane yanki na ƙasa, tana mai buƙatar gwamnati da ta tabbatar da kariya ga kowa ba tare da nuna bambanci ba.

 

“Idan ba mu magance irin waɗannan hare-haren ba, muna fuskantar barazanar ramuwar gayya da rarrabuwar ƙasa,” gidauniyar ta yi gargaɗi.

 

“Don ƙasarmu ta ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya, haɗin kai da jituwa, dole ne mu yi watsi da duk wani nau’in nuna wariya da tashin hankali.”

 

Wannan lamari ya haifar da gagarumar fusata a fadin ƙasa, tare da kiran ga gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo ƙarshen rikicin kabilanci da tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa.

Rel: Khadija Kubau

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara