Labarai
Karamar Hukumar Gwarzo Ta Kaddamar da Sabuwar Cibiyar Kiwon Lafiya
A wani muhimmin mataki na inganta harkar lafiya a matakin ƙasa, Karamar Hukumar Gwarzo ta kaddamar da sabuwar Cibiyar Kiwon Lafiya ta Farko (PHC) da aka gina a garin Dankado, da ke cikin gundumar Sabon Birni.
Taron kaddamarwar, wanda ke nuna wani sabon ci gaba a tsarin raya jama’a, ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, da wakilan al’umma.
Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo, Dakta Mani Tsoho Abdullahi, wanda Mataimakinsa, Alhaji Abdulmumin Garba Lakwaya, ya wakilta, ya tabbatar da jajircewar gwamnatin sa wajen tabbatar da cewa kowane yanki a cikin karamar hukumar na da damar samun ingantacciyar kiwon lafiya mai sauƙin samu da araha.
Ya yaba wa Kakakin Majalisar Dokoki ta Gwarzo, Ahmad Shehu Sabon Birni, da sauran kansiloli bisa hadin kai da jajircewarsu wajen aiwatar da muhimman ayyukan raya al’umma, yana mai cewa irin wannan haɗin gwiwa ita ce ginshiƙin ci gaban karkara mai dorewa.
A nasa jawabin, Ahmad Shehu Sabon Birni, ya bayyana sabuwar cibiyar lafiya a matsayin wata cibiya da za ta tallafawa jama’ar Dankado da makwabtansu. Ya jinjinawa karamar hukumar bisa mayar da hankali ga bangaren lafiya, tare da yin alkawarin ci gaba da ba da goyon bayan majalisa ga duk wani shiri da zai inganta rayuwar jama’a.
Shugaban sashen kula da kiwon lafiya na Gwarzo, Alhaji Tukur Makama, ya yaba da hangen nesa da jajircewar shugaban karamar hukumar wajen saka jari a fannin lafiyar jama’a. Ya ce sabuwar cibiyar za ta taimaka wajen rage mace-macen mata da jarirai, faɗaɗa rigakafi, da kuma samar da taimakon gaggawa ga al’umma cikin lokaci.
Shugabannin al’umma, ƙungiyoyin matasa da na mata, sun bayyana godiyarsu, suna mai cewa aikin ya zo a kan kari kuma ya dace da bukatun jama’a.
Rel/Khadijah Aliyu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
