Labarai
JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah
Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya bukaci Gwamnan jihar Niger, Umar Bago, da ya gaggauta sanya hannu kan dokar Hisbah da Majalisar Dokokin jihar ta amince da ita kwanan nan.
Sai dai Sheikh Jingir ya gargadi gwamnan da kada a mayar da batun dokar Hisbah zuwa siyasa, yana mai cewa dokar an tanade ta ne domin Musulmi, musamman ganin cewa kusan kashi 95 cikin 100 na al’ummar jihar Niger Musulmi ne.
Malamin ya bayyana hakan ne a wajen rufe tafsirin watan Ramadan na bana da aka gudanar a harabar gidan marigayi Malam Ladan a Minna, babban birnin jihar.
Ya jaddada cewa dokar Hisbah na inganta adalci, daidaito da gaskiya kamar yadda koyarwar addinin Musulunci ta tanada.
An wakilci Sheikh Jingir ne da Dr. Aliyu Ibrahim Shafi’i daga karamar hukumar Misau ta jihar Bauchi, wanda ya jagoranci tafsirin na shekara-shekara. Ya kuma kwantar wa wasu Kiristoci da ke nuna damuwa hankali, yana mai cewa a wasu lokuta har wasu ‘yan kabilar Igbo a jihar Bauchi kan kai kararrakinsu, har ma da matsalolin aure, gaban hukumar Hisbah domin a sasanta musu.
A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Malamai ta JIBWIS reshen jihar Niger, Sheikh Abubakar Abu Sumayyah, wanda Ustaz Muhammad Gulbin Sunnah ya wakilta, ya bayyana cewa dokar Hisbah ba wai domin cutar da kowa ba ce, yana mai kira ga jama’a su bayar da hadin kai domin ganin gwamnan ya sanya hannu a kanta cikin gaggawa.
Shi ma Shugaban Kwamitin Tafsir, Alhaji Ibrahim Dumus, wanda Alhaji Salisu Musa Koko ya wakilta, ya yaba wa tsohon shugaban mulkin soja Janar Ibrahim Babangida mai ritaya da kuma tsohon shugaban kasa Janar Abdulsalami Abubakar bisa goyon bayan da suka bayar ga tafsirin.
Ya kuma bayyana cewa kwamitin na shirin fara biyan kudin makaranta ga wasu marayu a makarantun firamare da sakandare a kananan hukumomin Bosso da Chanchaga na jihar.
A yayin taron, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Chanchaga, Malam Abdu Buba, ya bayar da gudunmawar naira miliyan daya, yayin da Shugaban karamar hukumar Chanchaga, Dr. Mustapha Jibrin Alheri, ya bayar da naira dubu dari biyar domin tallafa wa ayyukan kwamitin tafsirin.
Aliyu Lawal/Minna
-
Labarai6 days agoAn Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
-
Labarai6 days agoTinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa
-
Labarai6 days agoKwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara
-
Labarai4 days agoJami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi
-
Labarai4 days agoKwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara
-
Labarai4 days agoAn Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
-
Labarai4 days agoMatashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba
-
Labarai1 day ago‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa
