Labarai
Hukumar Lafiya a Kano ta Shirya Taron Masu Ruwa da Tsaki Kan Cutar Shan Inna
Daga Khadijah Aliyu
Hukumar Kula da Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Kano (KSPHCMB) ta gudanar da wani muhimmin taron game da shirye-shiryen tunkarar gamgamin wayar da kai kan allurar rigakafin cutar shan inna na watan Maris, a wani bangare na kokarin ci gaba da tabbatar da jihar ba ta da cutar tare da karfafa harkokin rigakafi na yau da kullum.
Taron, wanda aka gudanar a Cibiyar Ayyukan Gaggawa (EOC), ya hada manyan masu ruwa da tsaki, abokan hulda, da jami’an lafiya domin daidaita tsare-tsare da kuma karfafa hadin kai gabanin gudanar da shirin.
Yayin da yake jagorantar taron, Darakta Janar na KSPHCMB, Farfesa Salisu Ibrahim, ya jaddada muhimmancin hadin kai, da kuma sa hannun al’umma wajen tabbatar da nasarar shirin.
Ya bayyana cewa samun kyakkyawan sakamako na bukatar cikakken hadin gwiwa tsakanin dukkan bangarorin da ke da hannu a ayyukan rigakafi a fadin jihar.

Farfesa Ibrahim ya kuma jaddada bukatar fayyace ayyuka da nauyin da ya rataya a wuyan kowane bangare, ciki har da masu unguwanni, ma’aikatan lafiya, da sauran abokan hulda.
Ya ce hakan zai kara inganta gudanar da ayyuka tare da tabbatar da an kai ga jama’a da dama.
An kuma mai da hankali musamman kan rawar da Jami’an Rigakafi na Kananan Hukumomi (LIOs), Wakilan Unguwanni, Masu Ba da Shawara na Rukunoni, da Masu Sa-kai za su taka, musamman a fannonin wayar da kai, yin allurar rigakafi, da sa ido a matakin kasa.
Hukumar ta sake jaddada kudirinta na gudanar da ingantaccen shirin rigakafi mai tasiri ta hanyar karfafa hadin gwiwa da ci gaba da hada kan al’umma.
An kuma bukaci masu ruwa da tsaki da su kara kaimi wajen wayar da kai, tare da yin aiki tare domin tabbatar da cewa kowane yaro da ya cancanta ya samu allurar rigakafi.
Shirin watan Maris na daga cikin ci gaba da kokarin kawar da cutar shan inna da kuma inganta sakamakon rigakafi na yau da kullum a Jihar Kano.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
