Connect with us

Labarai

Hukumar Lafiya a Kano ta Shirya Taron Masu Ruwa da Tsaki Kan Cutar Shan Inna

Published

on

Daga Khadijah Aliyu

Hukumar Kula da Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Kano (KSPHCMB) ta gudanar da wani muhimmin taron game da shirye-shiryen tunkarar gamgamin wayar da kai kan allurar rigakafin cutar shan inna na watan Maris, a wani bangare na kokarin ci gaba da tabbatar da jihar ba ta da cutar tare da karfafa harkokin rigakafi na yau da kullum.

Taron, wanda aka gudanar a Cibiyar Ayyukan Gaggawa (EOC), ya hada manyan masu ruwa da tsaki, abokan hulda, da jami’an lafiya domin daidaita tsare-tsare da kuma karfafa hadin kai gabanin gudanar da shirin.

Yayin da yake jagorantar taron, Darakta Janar na KSPHCMB, Farfesa Salisu Ibrahim, ya jaddada muhimmancin hadin kai, da kuma sa hannun al’umma wajen tabbatar da nasarar shirin.

Ya bayyana cewa samun kyakkyawan sakamako na bukatar cikakken hadin gwiwa tsakanin dukkan bangarorin da ke da hannu a ayyukan rigakafi a fadin jihar.

Farfesa Ibrahim ya kuma jaddada bukatar fayyace ayyuka da nauyin da ya rataya a wuyan kowane bangare, ciki har da masu unguwanni, ma’aikatan lafiya, da sauran abokan hulda.

Ya ce hakan zai kara inganta gudanar da ayyuka tare da tabbatar da an kai ga jama’a da dama.

An kuma mai da hankali musamman kan rawar da Jami’an Rigakafi na Kananan Hukumomi (LIOs), Wakilan Unguwanni, Masu Ba da Shawara na Rukunoni, da Masu Sa-kai za su taka, musamman a fannonin wayar da kai, yin allurar rigakafi, da sa ido a matakin kasa.

Hukumar ta sake jaddada kudirinta na gudanar da ingantaccen shirin rigakafi mai tasiri ta hanyar karfafa hadin gwiwa da ci gaba da hada kan al’umma.

An kuma bukaci masu ruwa da tsaki da su kara kaimi wajen wayar da kai, tare da yin aiki tare domin tabbatar da cewa kowane yaro da ya cancanta ya samu allurar rigakafi.

Shirin watan Maris na daga cikin ci gaba da kokarin kawar da cutar shan inna da kuma inganta sakamakon rigakafi na yau da kullum a Jihar Kano.

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara