Connect with us

Labarai

Gwamnati: Farashin Kayan Abinci Na Raguwa, Tattalin Arziki Na Ingantuwa

Published

on

 

Gwamnatin Tarayya ta ce ‘yan Najeriya sun fara samun sauki yayin da farashin kayan abinci ke raguwa da farashin fetur ke daidaita, kuma naira ke karɓar ƙarfi.

 

Da yake magana a taron manema labarai na ministoci karo na huɗu a Abuja, Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohamed Idris, ya ce ci gaban, suna nuna cewa gyare-gyaren tattalin arziki na Shugaba Bola Tinubu na yin tasiri.

 

Ya amince da wahalhalun da ‘yan Najeriya suka sha amma ya tabbatar da cewa hakan ya fara wucewa.

 

Mohamed Idris ya ce Gwamnatin Tarayya tana nan daram wajen daidaita tattalin arziki da inganta rayuwar al’umma.

 

A jawabinsa, Ministan Ilimi, Dr. Maruf Alausa, ya ce kudaden da aka ware za su karfafa ilimin fasaha da sana’o’i a kasan nan.

 

Ya bayyana cewa za a samar da dakunan gwaji a manyan makarantu shida na koyar da aikin likitanci domin inganta horo. “Muna mai da hankali kan horo a aikace, musamman a fannin sauya injunan mota zuwa na CNG, kula da hasken rana, da kuma noma na zamani domin samar da karin ayyukan yi.”

 

Haka nan, Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya ce yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin Emirates da Air Peace za ta karfafa harkokin jiragen saman cikin gida.

 

Gwamnati na kuma aiwatar da sabbin manufofi don tallafawa kamfanonin jiragen saman cikin gida 13, domin su ci gaba da yin gogayya a da ire iren su a duniya.

 

Keyamo ya tabbatar da cewa an inganta tashoshin jiragen Hajj don kyautata tsarin aikin hajji.

 

A halin yanzu, Jami’ar Kimiyya da Fasahar Jiragen Sama ta Afirka ta fara aiki gaba ɗaya, kuma Najeriya ta rattaba hannu kan yarjejeniya da Boeing domin inganta sayan jirage da matakan tsaro.

 

A fannin amincewar kasa da kasa, tashoshin jirgin saman Port Harcourt da Abuja sun samu matsayi mafi kyau a Afirka dangane da tsaron fasinjoji da shirin gaggawa, a cewar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Duniya (ACI) a Afirka ta Kudu.

 

Radio Nigeria/Adamu

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara