Connect with us

Labarai

Gwamna Lawal Ya Buƙaci Masu Son Tsayawa Takara Su Aje Mukamansu

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal, ya umurci dukkan ‘yan majalisar zartaswar jihar da ke son takara a zaben shekarar 2027 da su ajiye mukamansu.

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a ranar Litinin yayin zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar a Gidan Gwamnati, Gusau.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, wannan umarni ya yi daidai da dokar zabe wacce Shugaban kasa ya rattaba hannu a kai, da kuma jadawalin zaben 2027 da hukumar zabe ta kasa INEC ta fitar.

Yau ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa na 64, inda aka tattauna muhimman batutuwa domin ci gaban Jihar Zamfara.

A jawabin bude zaman taron, gwamnan ya umurci dukkan mambobin majalisar zartarwar da ke neman mukaman siyasa su ajiye aikinsu kafin ko a ranar 31 ga watan Maris na shekarar 2026.”

Sanarwar ta ce, gwamnan ya umarci Sakataren Gwamnatin Jihar, da ya fitar da wata sanarwa ga dukkan jami’an gwamnati da ke da burin takara, wanda zai bukaci su ajiye mukamansu kafin ranar da aka kayyade.

Haka kuma, an umarci Shugaban Ma’aikata da ya aikawa dukkan ma’aikatan gwamnati da ke da niyyar yin takara domin su ajiye aikinsu.

Gwamna Lawal ya kara da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da mayar da hankali wajen hidimar al’ummar Jihar Zamfara.

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara