Labarai
Gwamna Lawal Ya Buƙaci Masu Son Tsayawa Takara Su Aje Mukamansu
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal, ya umurci dukkan ‘yan majalisar zartaswar jihar da ke son takara a zaben shekarar 2027 da su ajiye mukamansu.
Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a ranar Litinin yayin zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar a Gidan Gwamnati, Gusau.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, wannan umarni ya yi daidai da dokar zabe wacce Shugaban kasa ya rattaba hannu a kai, da kuma jadawalin zaben 2027 da hukumar zabe ta kasa INEC ta fitar.
“Yau ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa na 64, inda aka tattauna muhimman batutuwa domin ci gaban Jihar Zamfara.

“A jawabin bude zaman taron, gwamnan ya umurci dukkan mambobin majalisar zartarwar da ke neman mukaman siyasa su ajiye aikinsu kafin ko a ranar 31 ga watan Maris na shekarar 2026.”
Sanarwar ta ce, gwamnan ya umarci Sakataren Gwamnatin Jihar, da ya fitar da wata sanarwa ga dukkan jami’an gwamnati da ke da burin takara, wanda zai bukaci su ajiye mukamansu kafin ranar da aka kayyade.

Haka kuma, an umarci Shugaban Ma’aikata da ya aikawa dukkan ma’aikatan gwamnati da ke da niyyar yin takara domin su ajiye aikinsu.
Gwamna Lawal ya kara da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da mayar da hankali wajen hidimar al’ummar Jihar Zamfara.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
