Connect with us

Labarai

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Published

on

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka Offor Foundation, a wani ɓangare na shirin ƙasa baki ɗaya na ƙarfafa horaswa da bincike a cibiyoyin lafiya na tarayya.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na cibiyar, Dakta Naziru A. Tukur ya fitar, ya ce tallafin na daga cikin wani babban shirin rabon littattafai da ya shafi cibiyoyin lafiya 58 da aka zaɓa a faɗin yankuna shida na ƙasar.

Dakta Tukur ya bayyana cewa an tanadi littattafan ne domin tallafa wa koyarwa, horas da ƙwararru da kuma bincike a cibiyoyin da suka amfana.

Ya ƙara da cewa gidauniyar ta ɗauki nauyin sayo da jigilar kwantena goma na littattafai da mujallu na zamani masu tsawon kafa 40 zuwa Najeriya domin aiwatar da shirin.

Wannan rabon littattafai shi ne karo na 13 na shirin da aka fara tun a shekarar 2013. Ba kamar lokutan baya ba, na shekarar 2026 ya mayar da hankali ne kacokan kan fannin kiwon lafiya.

A cikin wasiƙar da aka aika wa Daraktan Lafiya na cibiyar, Dakta Bello A. Mohammed, gidauniyar ta ce wannan tallafi ya biyo bayan buƙatar da Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a mai kula da harkokin daidaitawa, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya gabatar a madadin cibiyoyin lafiya na tarayya.

Wasiƙar wadda mukaddashin Babban Jami’in Ma’aikata na gidauniyar, Barista Chijioke James ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa an amince da sayo da jigilar littattafan daga Amurka domin ƙara ƙarfafa horaswa a cibiyoyin lafiya na ƙasar.

Ta kuma nuna cewa Cibiyar ta Gusau na daga cikin cibiyoyin da aka zaɓa su ci gajiyar shirin.

Da yake mayar da martani, Daraktan Lafiya na cibiyar, Dakta Bello A. Mohammed, ya gode wa gidauniyar da kuma ministan bisa wannan tallafi na kan lokaci.

Ya ce gudunmawar za ta taimaka matuƙa wajen bunƙasa harkokin ilimi da ƙwarewa a cibiyar, musamman a daidai lokacin da ake ƙoƙarin mayar da ita asibitin koyarwa.

Dakta Mohammed ya kuma yi kira ga masu hannu da shuni, ’yan kasuwa, ’yan siyasa, shugabannin addini da na gargajiya da sauran jama’a da su yi koyi da wannan kyakkyawan aiki na taimako.

Ya jaddada cewa ci gaba da tallafi daga masu ruwa da tsaki yana da muhimmanci wajen haɓaka cibiyar da kuma inganta ayyukan kula da lafiya.

“Babu wanda ya kai talauci da ba zai iya bayarwa ba, kamar yadda babu wanda ya kai arziki da ba zai iya karɓa ba,” in ji shi, yana mai tabbatar da cewa za a yi amfani da littattafan yadda ya kamata domin inganta koyarwa da kuma ingancin ayyukan kiwon lafiya.

A gefe guda kuma, cibiyar ta kafa wani kwamiti domin tantance littattafan da kuma gano bukatun sassa daban-daban, domin tabbatar da an raba su yadda ya dace.

Shugaban kwamitin kuma Mataimakin Shugaban Sashen Ayyukan Asibiti (Bincike da Horaswa), Dakta Usman Sulaiman, ya ce sun fara aikin tantance littattafan gaba ɗaya.

Ya bayyana cewa za a rarraba littattafan bisa fannoni da muhimmanci, sannan a duba gibin da ke akwai a sassa da ɗakunan karatu daban-daban.

Ya ƙara da cewa kwamitin na shirin kafa tsarin bibiyar amfani da littattafan da kula da su, domin tabbatar da an kiyaye su yadda ya kamata kuma ma’aikata suna samun sauƙin amfani da su.

Aminu Dalhatu

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara