Labarai
FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor
Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka Offor Foundation, a wani ɓangare na shirin ƙasa baki ɗaya na ƙarfafa horaswa da bincike a cibiyoyin lafiya na tarayya.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na cibiyar, Dakta Naziru A. Tukur ya fitar, ya ce tallafin na daga cikin wani babban shirin rabon littattafai da ya shafi cibiyoyin lafiya 58 da aka zaɓa a faɗin yankuna shida na ƙasar.
Dakta Tukur ya bayyana cewa an tanadi littattafan ne domin tallafa wa koyarwa, horas da ƙwararru da kuma bincike a cibiyoyin da suka amfana.
Ya ƙara da cewa gidauniyar ta ɗauki nauyin sayo da jigilar kwantena goma na littattafai da mujallu na zamani masu tsawon kafa 40 zuwa Najeriya domin aiwatar da shirin.
Wannan rabon littattafai shi ne karo na 13 na shirin da aka fara tun a shekarar 2013. Ba kamar lokutan baya ba, na shekarar 2026 ya mayar da hankali ne kacokan kan fannin kiwon lafiya.
A cikin wasiƙar da aka aika wa Daraktan Lafiya na cibiyar, Dakta Bello A. Mohammed, gidauniyar ta ce wannan tallafi ya biyo bayan buƙatar da Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a mai kula da harkokin daidaitawa, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya gabatar a madadin cibiyoyin lafiya na tarayya.
Wasiƙar wadda mukaddashin Babban Jami’in Ma’aikata na gidauniyar, Barista Chijioke James ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa an amince da sayo da jigilar littattafan daga Amurka domin ƙara ƙarfafa horaswa a cibiyoyin lafiya na ƙasar.
Ta kuma nuna cewa Cibiyar ta Gusau na daga cikin cibiyoyin da aka zaɓa su ci gajiyar shirin.
Da yake mayar da martani, Daraktan Lafiya na cibiyar, Dakta Bello A. Mohammed, ya gode wa gidauniyar da kuma ministan bisa wannan tallafi na kan lokaci.
Ya ce gudunmawar za ta taimaka matuƙa wajen bunƙasa harkokin ilimi da ƙwarewa a cibiyar, musamman a daidai lokacin da ake ƙoƙarin mayar da ita asibitin koyarwa.
Dakta Mohammed ya kuma yi kira ga masu hannu da shuni, ’yan kasuwa, ’yan siyasa, shugabannin addini da na gargajiya da sauran jama’a da su yi koyi da wannan kyakkyawan aiki na taimako.
Ya jaddada cewa ci gaba da tallafi daga masu ruwa da tsaki yana da muhimmanci wajen haɓaka cibiyar da kuma inganta ayyukan kula da lafiya.
“Babu wanda ya kai talauci da ba zai iya bayarwa ba, kamar yadda babu wanda ya kai arziki da ba zai iya karɓa ba,” in ji shi, yana mai tabbatar da cewa za a yi amfani da littattafan yadda ya kamata domin inganta koyarwa da kuma ingancin ayyukan kiwon lafiya.
A gefe guda kuma, cibiyar ta kafa wani kwamiti domin tantance littattafan da kuma gano bukatun sassa daban-daban, domin tabbatar da an raba su yadda ya dace.
Shugaban kwamitin kuma Mataimakin Shugaban Sashen Ayyukan Asibiti (Bincike da Horaswa), Dakta Usman Sulaiman, ya ce sun fara aikin tantance littattafan gaba ɗaya.
Ya bayyana cewa za a rarraba littattafan bisa fannoni da muhimmanci, sannan a duba gibin da ke akwai a sassa da ɗakunan karatu daban-daban.
Ya ƙara da cewa kwamitin na shirin kafa tsarin bibiyar amfani da littattafan da kula da su, domin tabbatar da an kiyaye su yadda ya kamata kuma ma’aikata suna samun sauƙin amfani da su.
Aminu Dalhatu
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
