Labarai
An Warware Rikicin Shugabancin Da Ya Dabaibaye Kungiyar Likitocin Zamfara
Kwamishinan lafiya na jihar Zamfara, Dr. Nafisa Muhammad Maradun, ta warware rikicin shugabancin kungiyar likitocin Najeriya NMA reshen jihar Zamfara.
Jami’in yada labarai, ma’aikatar lafiya. Sulaiman Isa ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar. Ya ce; Maradun tana magana ne a lokacin da ta karbi bakuncin kungiyar dattawan kungiyar reshen jihar Zamfara karkashin jagorancin Dr. Hassan Mamman a ziyarar ban girma da ya kai.
Kungiyar dattawan ta yaba da jajircewar Dr. Maradun da hangen nesa wajen jagorantar kungiyar likitocin Najeriya ta jaha a wannan lokaci mai cike da kalubale.
Taron ya kuma yi tsokaci kan tasirin sa hannun ta ga kungiyar da kuma tsarin kiwon lafiya baki daya a jihar.
Dakta Nafisa Maradun ta jaddada fifikon inganta fannin lafiya bisa tsarin ceton lafiyar al’umma na Gwamna Dauda Lawal.
Ta nuna jin dadinta da ziyarar kungiyar dattawan tare da jaddada kudurin yin aiki kafada da kafada da kungiyar likitocin domin cimma manufofin shirin ceto.
Ziyarar na nuna wani gagarumin mataki na karfafa hadin gwiwa tsakanin ma’aikatar lafiya da kwararrun likitoci a jihar.
REL/AMINU DALHATU/Wababe
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
