Connect with us

Ilimi

Babu Gaskiya Ga Labarin Rashin Ingancin Makarantun Jihar Nasarawa – Peter

Published

on

Gwamnatin Nasarawa ta karyata labarin da wata kafar yada labarai ta wallafa akan rashin ingancin kayan karatu a jihar.

 

Gwamnatin jihar nasarawa tace babu kamshin gaskiya a cikin rahoton da wara kafar yada labarai ta wallafa cewar yaran ‘yan-makarantan firamaren gwamnati suna karatu a kasa babu kujeru.

 

Rahoton bayanma babu labarin gaskiya da aka rubuta gwamnatin jihar na zargin an dauki nauyin kafar yada labarai ne domin yin adawa da ayyukan raya jihar da gwamnati maici ke gudanarwa a faɗin jihar, musamma ma a bangaren ilimi.

 

A wata sanarwa da mataimakin na musamman akan harkokin al’umma mista Peter Ahemba ya rabawa manema labarai a lafiya yace gaskiya ne wasu makarantu suna fama da karancin kayayyakin koyo dana koyarwa a wasu makarantu a jihar kamar yadda yake a kasashe masu tasowa, gwamnatin jihar nasarawa ta dauki kwararan matakai wajen samar da dukkannin ababen da ake bukata a sashin koyo dana koyarwa, gyaran makarantu, Gina wasu sabbi harma da samar kujerun zama ga dalibai da dai-dai sauransu.

 

Sanarwan tayi bayanin cewar ko a kwanakin Gwamnan jihar nasarawa Abdullahi Sule ta hannun hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar ya raba daruruwan kujerun zama dana rubutu dama takardun rubutu da karatu a faɗin jihar.

 

Sanarwan ta kara da cewar, gwamnatin jihar zata cigaba da katange makarantu ta na firamare da sakandare hadi giggina fanfunan burtsatse dama Sauran ababen more rayuwa domin ‘ya’yansu Daman karatu cikin inganci da natsuwa.

 

Hakazalika, ta bukaci al’umma da suyi watsi da wannan rahoton da cewar baida tushe balle makama, inda ta hori ‘yan-jaridu da a koda yaushe kafin su wallafa labarinsu su tabbatar sunyi cikakken bincike a hannun jami’an gwamnati domin gudun yada labarai kanzon kurege.

 

Kana sanarwan ta bada tabbacin gwamnatin jihar nasarawa wajen samar da dukkannin ababen da ake bukata don inganta ilimi hadi da bunkasa walwalan malamai basu horo, daukan wasu sabbi malamai aiki dama cigaba da biyan albashi akan lokaci.

Rel/Aliyu Muraki/lafiya.

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara