Ilimi
Babu Gaskiya Ga Labarin Rashin Ingancin Makarantun Jihar Nasarawa – Peter
Gwamnatin Nasarawa ta karyata labarin da wata kafar yada labarai ta wallafa akan rashin ingancin kayan karatu a jihar.
Gwamnatin jihar nasarawa tace babu kamshin gaskiya a cikin rahoton da wara kafar yada labarai ta wallafa cewar yaran ‘yan-makarantan firamaren gwamnati suna karatu a kasa babu kujeru.
Rahoton bayanma babu labarin gaskiya da aka rubuta gwamnatin jihar na zargin an dauki nauyin kafar yada labarai ne domin yin adawa da ayyukan raya jihar da gwamnati maici ke gudanarwa a faɗin jihar, musamma ma a bangaren ilimi.
A wata sanarwa da mataimakin na musamman akan harkokin al’umma mista Peter Ahemba ya rabawa manema labarai a lafiya yace gaskiya ne wasu makarantu suna fama da karancin kayayyakin koyo dana koyarwa a wasu makarantu a jihar kamar yadda yake a kasashe masu tasowa, gwamnatin jihar nasarawa ta dauki kwararan matakai wajen samar da dukkannin ababen da ake bukata a sashin koyo dana koyarwa, gyaran makarantu, Gina wasu sabbi harma da samar kujerun zama ga dalibai da dai-dai sauransu.
Sanarwan tayi bayanin cewar ko a kwanakin Gwamnan jihar nasarawa Abdullahi Sule ta hannun hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar ya raba daruruwan kujerun zama dana rubutu dama takardun rubutu da karatu a faɗin jihar.
Sanarwan ta kara da cewar, gwamnatin jihar zata cigaba da katange makarantu ta na firamare da sakandare hadi giggina fanfunan burtsatse dama Sauran ababen more rayuwa domin ‘ya’yansu Daman karatu cikin inganci da natsuwa.
Hakazalika, ta bukaci al’umma da suyi watsi da wannan rahoton da cewar baida tushe balle makama, inda ta hori ‘yan-jaridu da a koda yaushe kafin su wallafa labarinsu su tabbatar sunyi cikakken bincike a hannun jami’an gwamnati domin gudun yada labarai kanzon kurege.
Kana sanarwan ta bada tabbacin gwamnatin jihar nasarawa wajen samar da dukkannin ababen da ake bukata don inganta ilimi hadi da bunkasa walwalan malamai basu horo, daukan wasu sabbi malamai aiki dama cigaba da biyan albashi akan lokaci.
Rel/Aliyu Muraki/lafiya.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
