Connect with us

Labarai

Adalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari

Published

on

Masu ruwa da tsaki daga masarautun gargajiya na Kumana da Chawai a Karamar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna sun amince da wani tsarin raba mukamai na siyasa da nufin magance rashin daidaito da aka dade ana fama da shi a yankin.

Wannan matsaya ta samu ne bayan tarurrukan da aka gudanar a ranakun 26 da 27 ga watan Maris, 2026, inda aka gabatar da shawarar juyawar mukamai na siyasa tsakanin manyan rukuni uku na yankin, wato Masarautar Kauru, Masarautar Kumana da Masarautar Chawai.

A karkashin wannan tsari, an ware kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya ga Masarautar Kauru, kujerar Majalisar Dokokin Jiha ga Masarautar Chawai, yayin da kujerar Shugaban Karamar Hukuma aka bai wa Masarautar Kumana.

Masu ruwa da tsaki daga Kumana da Chawai sun yaba da rawar da dattawan al’umma, tsofaffin jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki suka taka a tattaunawar, suna mai cewa wannan mataki wani yunkuri ne na gina hadin kai da zaman lafiya a Kauru.

Sai dai, wannan matsaya ta jawo suka daga wani bangare na masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar APC a yankin.

Wannan bangare, karkashin jagorancin wani Zakka Peter da S.M. Taggah, ya nuna adawa da tsarin raba mukaman, inda suka goyi bayan sake zaben tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya, Muktar Zakari Chawai, da kuma dan majalisar dokokin jiha, Haruna Barnabas Danmaigona.

Sun bayyana cewa ya kamata a bar zabin shugabanni ga muradin jama’a ta hanyar dimokuradiyya maimakon tsarin raba mukamai.

A martaninsu, kungiyar KYA, wato  Kauru Youth Ambassadors wanda Junaidu Ishaq Maisalati ke jagoranta ta jaddada cewa tsarin raba mukamai hanya ce halal a dimokuradiyya domin tabbatar da adalci da hana wata kabila ko bangare mamaye iko.

Sun kuma yi nuni da sakamakon zaben 2023, inda suka ce sakamakon ya nuna yadda jama’a ke kallon yadda shugabanci ya gudana a yankin.

KYA ta yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a Karamar Hukumar Kauru da su fifita hadin kai da cigaban al’umma gaba daya fiye da muradun bangarori.

Har ila yau, ta bukaci Gwamnatin Jihar Kaduna da ta mara baya ga shirye-shiryen da ke inganta hadin kai da tabbatar da adalci wajen shiga harkokin siyasa.

Kungiyar ta jaddada cewa wannan tsarin raba mukamai shi ne matakin farko na kokarin karfafa dimokuradiyya da tabbatar da daidaitaccen wakilci a Kauru.

Daga: Yusuf Zubairu

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara