Labarai
Jinkirin Fansho: PTAD Ta Fadi Dalili, Ta Ce Za a Biya Kudaden Wannan Wata
Hukumar kula da shirye-shiryen fansho na wucin gadi, wato PTAD, ta nemi afuwar ’yan fansho a fadin Najeriya kan jinkirin biyan wasu daga cikin kudaden fansho da suka taru.
A wata tattaunawa ta waya da Shugaban Kungiyar Tsofaffin Ma’aikatan NIPOST na reshen Jihar Legas, Kwamared Mukaila Ogunbote, jami’an PTAD sun bayyana cewa jinkirin ya samo asali ne daga wasu matsaloli da suka shafi Babban Bankin Najeriya da kuma Ma’aikatar Kudi.
Sai dai hukumar ta tabbatar da cewa dukkan hakkokin da suka rage, ciki har da na wadanda aka sake rijista bayan tantancewar “Ina Raye”, za a biya su a cikin wannan watan.
Kwamared Ogunbote ya ce an tattauna batutuwa da dama da suka shafi walwalar ’yan fansho, kuma ya sha alwashin ci gaba da bibiyar lamarin har sai an warware matsalolin da ke tattare da shi.
Ya kuma roki hadin kai, fahimta da juriya daga tsofaffin ma’aikatan, domin a cimma mafita cikin ruwan sanyi, musamman ganin cewa Shugaba Bola Tinubu ya amince da sakin naira biliyan sittin da takwas domin biyan bashin.
Suleiman Kaura
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
