Connect with us

Labarai

Salon ‘yan sanda da sojoji na ba ni takaici a yaki da ’yan bindiga – Gwamnan Zamfara

Published

on

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya koka kan yadda ’yan sanda da sojoji suka sanya sakaci a yaƙi da ’yan bindiga a shiyyar Arewa maso Yamma.

Gwamna Lawal bayyana haka ne a wani jawabi kai tsaye da ya gabatar cikin a shirin SUNRISE DAILY na gidan talabijin na CHANNELS TV a ranar Talatar nan.

Ya ce, irin salon hukumomin tsaron Gwamnatin Tarayya ya sa aka samar da Rundunar Tsaron Jihar masu suna ‘Askarawan Zamfara’.

Gwamna Dauda Lawal ya ce, “Mu a matsayin mu na gwamnoni, ba mu da iko a kan sojoji, ba mu da iko a kan ’yan sanda da jami’an tsaron farin kaya, shi ya sa galibi abin ke sa mu cikin damuwa.

“Za ka ga a lokacin da muke buƙatar waɗannan dakarun tsaro, ba za a same su ba, bisa haka ne muka ga mafita kawai mu kafa rundunar mu ta kanmu.”

Gwamnan ya bayyana cewa za a iya magance ‘yan bindiga, waɗanda suka mayar da garkuwa da mutane sana’a, cikin makonni biyu idan aka yi niyyar hakan.

“A mako biyu za su zama tarihi amma ba a shirya hakan ba a siyasance, mun san su waye ’yan bindigar nan kuma mun san wurin da suke rayuwa,” inji Dauda Lawal.

Gwamna Lawal ya yi zargin cewa wasu abokan hamayyarsa na siyasa suna tattaunawa da ’yan bindiga ba da saninsa ba.

Lokacin da aka tambaye shi ko ya san ainihin waɗanda ke tattaunawa da ‘yan bindigar, sai ya ce, “Duk abin da suke yi mun sani.”

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara