Connect with us

Fasaha

An sami Ci gaba a bangaren Sufuri – Farfesa Umar

Published

on

Shugaban Jami’ar Sufuri ta Gwamnatin Tarayya dake Daura Jahar Katsina Farfesa Umar Adam Katsayal ya bayyana haka yayin zantawarshi da Radio Nigeria Kaduna.

A cewar Farfesa Umar Adam Katsayal kafin samun ‘Yan cin kai hanyoyin Mota hanya daya ne ba tagwayen hanyoyi ba sai bayan samun ‘yan cin kai aka fara samar da tagwayen hanyoyi tare ma da samun hanyoyin Mota da Suka hada garuruwa baya ga samun hanyoyin gadojin Mota na sama a manyan garuruwa da biranen kasa, hakama ta bangaren Filayen Jiragen Sama.

Shugaban Jami’ar Sufurin ya bayyana cewa kafin samun ‘yan cin kai sai a Birnin Ikko da Kano ake da tashoshin sauka da tashin Jiragen Sama da a yanzu kusan Jahohin wannan kasa ke da tashoshin sauka da tashin Jiragen Sama dama kokarin Samar da tashoshin Jiragen sama na dakon kaya.

Da ya juwa ta bangaren Sufurin tashoshin ruwa ya bayyana yadda ake dakon kaya daga wasu kasashe zuwa Nijeriya a tashoshin ruwa tare ma da samar da hanyoyin Jiragen kasa fiye da wadanda turawan mulkin mallaka suka bari da yanzu ma ake kokarin hada titin Jirgin kasa zuwa Jamhuriyar Niger baya ga tashoshin kan tudu da ake dako da sauke kaya.

Farfesa Umar Adam Katsayal ya bayyana ci gaba da aka samu a fannin Sufuri ta hanyar samar da Jami’ar Sufurin ta Gwamnatin Tarayya dake Daura domin inganta harkokin Sufuri a Nigeria da wannan Jami’a ita ce Jami’a irin ta ta farko a Nahiyar Africa.

A karshe Shugaban Jami’ar Sufurin ta Gwamnatin Tarayya dake Daura Farfesa Umar Adam Katsayal ya taya Shugaban kasa Bola Tinubu murnar cikar Nigeria Shekaru 65 da samun ‘yan cin kai da Mataimakinshi hadi da Shugabannin Majalisun Tarayyar Nigeria da Ministocin Sufuri da Ilmi a Tarayya Nigeria dama daukacin al’ummar Nigeria tare da kira ga ‘yan Kasa na ci gaba da yiwa Nigeria addu’o’in samun ci gaba da habakar tattalin arziki dama samun tsaro da zaman lafiya.

Ibrahim Idris Kaura Namoda/Kaduna

Labarai

Labarai38 minutes ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Aikin Ban-ruwa

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai20 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara