Fasaha
An sami Ci gaba a bangaren Sufuri – Farfesa Umar
Shugaban Jami’ar Sufuri ta Gwamnatin Tarayya dake Daura Jahar Katsina Farfesa Umar Adam Katsayal ya bayyana haka yayin zantawarshi da Radio Nigeria Kaduna.
A cewar Farfesa Umar Adam Katsayal kafin samun ‘Yan cin kai hanyoyin Mota hanya daya ne ba tagwayen hanyoyi ba sai bayan samun ‘yan cin kai aka fara samar da tagwayen hanyoyi tare ma da samun hanyoyin Mota da Suka hada garuruwa baya ga samun hanyoyin gadojin Mota na sama a manyan garuruwa da biranen kasa, hakama ta bangaren Filayen Jiragen Sama.
Shugaban Jami’ar Sufurin ya bayyana cewa kafin samun ‘yan cin kai sai a Birnin Ikko da Kano ake da tashoshin sauka da tashin Jiragen Sama da a yanzu kusan Jahohin wannan kasa ke da tashoshin sauka da tashin Jiragen Sama dama kokarin Samar da tashoshin Jiragen sama na dakon kaya.
Da ya juwa ta bangaren Sufurin tashoshin ruwa ya bayyana yadda ake dakon kaya daga wasu kasashe zuwa Nijeriya a tashoshin ruwa tare ma da samar da hanyoyin Jiragen kasa fiye da wadanda turawan mulkin mallaka suka bari da yanzu ma ake kokarin hada titin Jirgin kasa zuwa Jamhuriyar Niger baya ga tashoshin kan tudu da ake dako da sauke kaya.
Farfesa Umar Adam Katsayal ya bayyana ci gaba da aka samu a fannin Sufuri ta hanyar samar da Jami’ar Sufurin ta Gwamnatin Tarayya dake Daura domin inganta harkokin Sufuri a Nigeria da wannan Jami’a ita ce Jami’a irin ta ta farko a Nahiyar Africa.
A karshe Shugaban Jami’ar Sufurin ta Gwamnatin Tarayya dake Daura Farfesa Umar Adam Katsayal ya taya Shugaban kasa Bola Tinubu murnar cikar Nigeria Shekaru 65 da samun ‘yan cin kai da Mataimakinshi hadi da Shugabannin Majalisun Tarayyar Nigeria da Ministocin Sufuri da Ilmi a Tarayya Nigeria dama daukacin al’ummar Nigeria tare da kira ga ‘yan Kasa na ci gaba da yiwa Nigeria addu’o’in samun ci gaba da habakar tattalin arziki dama samun tsaro da zaman lafiya.
Ibrahim Idris Kaura Namoda/Kaduna
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
