Labarai
Shugaba Tinubu Ya Karbi Bukuncin Takwaransa Na Saliyo
A yau Litinin ne shugaba Bola Tinubu ya karbi bakuncin takwaransa na Saliyo, Julius Maada Bio a fadar gwamnati da ke Abuja.
Da isarsa, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila ya tarbe shi, kafin ya kai ziyarar ban girma da shugaba Tinubu, wanda kuma ke rike da mukamin shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS.
Wakilin gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa shugabannin biyu sun yi ganawar sirri, duk da cewa har yanzu ba a bayyana cikakken bayanin tattaunawar da suka yi ba.
Wannan ita ce ziyarar girmamawa ta farko da Shugaba Bio ya kai wa Shugaba Tinubu. Duk da haka, ya kasance cikin mahalarta taron ECOWAS da aka rika gudanar a Abuja karkashin jagorancin Najeriya.
Daga Bello Wakili
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
