Ilimi
Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British
Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon yadda wata ɗaliba ke cin zalin ƴar ajinsu ya bazu a shafukan sada zumunta.
Kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta ce rundunar ta san da abin da ya faru kuma tana ɗaukan mataki a kai.
A cewar kakakin, ƴan sandan da aka tura za su gudanar da bincike tare da hana karya doka da oda.
A ranar Litinin ne bidiyon da ke nuna yadda ake cin zalin wata ɗaliba ya karaɗe shafukan sada zumunta lamarin da ya fusata al’ummar kasan nan.
Tuni dai hukumar makarantar ta fitar da sanarwa inda ta nemi yafiyar al’umma da kuma iyayen ɗaliban makarantar sannan ta ce ta soma bincike kan lamarin.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
