Connect with us

Kasuwanci

’Yan Bindiga Sun Kai Hari Kauyukan Katsina, Sun Kashe Mutane 8

Published

on

’Yan bindiga sun kai hari wasu ƙauyuka huɗu a Ƙaramar Hukumar Dandume ta Jihar Katsina, inda suka kashe mutane takwas tare da jikkata wasu mutum goma sha ɗaya da raunuka mabambanta.

Maharan, waɗanda suka kai harin a ƙauyukan Baraje, Kirijan, Shugu, Kauran Pawa da Unguwar Jika da tsakar dare, sun kuma yi garkuwa da mutum guda tare da lalata gidaje da wuraren kasuwanci.

Yayin da ba a samu jin ta bakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar domin tabbatar da faruwar lamarin ba, majiyoyi da dama daga al’ummomin da abin ya shafa sun tabbatar wa Rediyon Najeriya aukuwar harin.

Wani mazaunin Baraje, Malam Nura, ya shaida wa Rediyon Najeriya ta wayar tarho cewa maharan sun shiga ƙauyen da misalin ƙarfe goma sha biyu na dare, inda suke haska fitilu tare da harba bindiga ba kakkautawa cikin gidajen mutane.

Ya bayyana cewa an riga an binne gawarwakin waɗanda suka rasu, yayin da ake ci gaba da ba wa waɗanda suka jikkata kulawar lafiya a Babban Asibitin Funtua.

Mazauna yankin sun nuna takaicinsu kan harin, inda suka ce hakan ya saɓa wa yarjejeniyar zaman lafiya da aka cim ma a bara tsakanin ’yan bindiga da al’ummomin yankin, wadda kowanne ɓangare ya ɗauki alƙawarin ɗaukar matakan da za su ƙarfafa zaman lafiya.

Isma’il Adamu

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara