Connect with us

Labarai

Rundunar ‘Yansandan Kabi Ta Tabbatar da Mutuwar Mutane 33 Sakamakon Fashi da Makami

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kebbi ta ƙara tsaurara matakan tsaro a Gundumar Bui da ke Ƙaramar Hukumar Arewa, bayan wani hari na satar shanu da ya auku a ranar Larabar da ta gabata.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Sanarwar ta ce an tura ƙarin jami’an tsaro da kayan aiki na musamman zuwa yankin, yayin da ake ci gaba da sintiri domin tabbatar da zaman lafiya. Rundunar ta nuna alhini matuƙa kan mutuwar mutane 33 marasa laifi, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan da daukacin al’ummar Arewa.

Binciken farko ya nuna cewa wasu ‘yan bindiga da ake kira Lakurawa ne suka shiga yankin domin satar shanu, kuma ana zargin sun tsallaka ne daga Ƙaramar Hukumar Gudu ta Jihar Sokoto.

Mutanen da abin ya shafa sun fito ne daga garuruwan Mamunu, Awasaka, Tungan Tsoho, Makangara, Kanzo, Gorun Naidal da Dan Mai Ago, inda suka yi yunƙurin mayar da martani, wanda a yayin haka ne aka yi mummunar arangama da ta yi sanadin asarar rayuka.

Rundunar ta jaddada cewa duk wani lamari da ya shafi ‘yan ta’adda masu makami na buƙatar haɗin kai da hukumomin tsaro. Don haka ta buƙaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani motsi mai tayar da hankali ta hanyoyin tsaro da aka tanada, maimakon su ɗauki mataki da kansu, domin irin waɗannan arangama na da matuƙar haɗari.

Ta kuma bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan musamman domin kamo waɗanda suka aikata laifin, hana sake aukuwar irin haka, da kuma ƙarfafa hanyoyin samar da bayanan gaggawa.

Rundunar ta bayar da lambobin wayar ɗakin kula da bayanai kamar haka: 08038797644 da 09015888578 domin kai rahoto cikin gaggawa.

REL SANI DUTSINMA

Labarai

Ilimi14 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara