Connect with us

Labarai

Rundunar ‘Yansandan Kabi Ta Tabbatar da Mutuwar Mutane 33 Sakamakon Fashi da Makami

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kebbi ta ƙara tsaurara matakan tsaro a Gundumar Bui da ke Ƙaramar Hukumar Arewa, bayan wani hari na satar shanu da ya auku a ranar Larabar da ta gabata.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Sanarwar ta ce an tura ƙarin jami’an tsaro da kayan aiki na musamman zuwa yankin, yayin da ake ci gaba da sintiri domin tabbatar da zaman lafiya. Rundunar ta nuna alhini matuƙa kan mutuwar mutane 33 marasa laifi, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan da daukacin al’ummar Arewa.

Binciken farko ya nuna cewa wasu ‘yan bindiga da ake kira Lakurawa ne suka shiga yankin domin satar shanu, kuma ana zargin sun tsallaka ne daga Ƙaramar Hukumar Gudu ta Jihar Sokoto.

Mutanen da abin ya shafa sun fito ne daga garuruwan Mamunu, Awasaka, Tungan Tsoho, Makangara, Kanzo, Gorun Naidal da Dan Mai Ago, inda suka yi yunƙurin mayar da martani, wanda a yayin haka ne aka yi mummunar arangama da ta yi sanadin asarar rayuka.

Rundunar ta jaddada cewa duk wani lamari da ya shafi ‘yan ta’adda masu makami na buƙatar haɗin kai da hukumomin tsaro. Don haka ta buƙaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani motsi mai tayar da hankali ta hanyoyin tsaro da aka tanada, maimakon su ɗauki mataki da kansu, domin irin waɗannan arangama na da matuƙar haɗari.

Ta kuma bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan musamman domin kamo waɗanda suka aikata laifin, hana sake aukuwar irin haka, da kuma ƙarfafa hanyoyin samar da bayanan gaggawa.

Rundunar ta bayar da lambobin wayar ɗakin kula da bayanai kamar haka: 08038797644 da 09015888578 domin kai rahoto cikin gaggawa.

REL SANI DUTSINMA

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara