Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Nasarawa Ta Roki Malaman Jami’o’i Masu Yajin Aiki Su Koma Aji – SSA Ahemba

Published

on

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi kira ga malaman manyan makarantu mallakar jihar da ke yajin aiki da su janye yajin aikin da suke gudanarwa, domin bai wa tattaunawa damar ci gaba don warware matsalolin da ke haddasa rikicin cikin gaggawa.

Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan Harkokin Jama’a, Mista Peter Ahemba, ne ya yi wannan roko yayin da yake jawabi ga ’yan jarida a taron manema labarai na watanni biyu-biyu da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Mista Ahemba ya ce yajin aikin da Malaman Kwalejin Ilimi ta Akwanga da kwalejin kimiyya da fasaha ta Isa Mustapha Agwai Lafia, da Kwalejin Aikin Noma, Kimiyya da Fasaha ta Lafia ke yi na iya kawo cikas ga karatun dalibai. Saboda haka, ya roki ƙungiyoyin malaman da su koma teburin tattaunawa domin cimma matsaya cikin lumana.

Ƙungiyoyin Malaman Manyan Makarantu na Jihar Nasarawa sun ayyana yajin aikin sai baba-ta-gani a ranar 29 ga Disamba, 2025, bisa rashin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa ga mambobinsu.

Babban Mataimakin na Musamman ya bayyana cewa kwanan nan Gwamna Abdullahi Sule ya raba katifa dubu ɗaya da gadaje ga daliban Kwalejin Ilimi ta Akwanga (COEA), domin inganta muhallin koyo da koyarwa.

Ya ce wannan rabon na daga cikin kulawar da gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule ke bai wa fannin ilimi tun daga lokacin da ta hau mulki a shekarar 2019.

Mista Ahemba ya ƙara da cewa gwamnatin ta gina azuzuwa da dama, ta gyara makarantu masu yawa, tare da gina katangar kariya a makarantu da dama domin kare su daga mamaya.

Ya kuma ce gwamnatin ta fahimci yadda wasu miyagun mutane ke shiga jihar a hankali, lamarin da ke barazana ga tsaron mazauna yankin.

Mista Ahemba ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin tsakar dare da wasu da ba a tantance su ba suka kai wa mazauna Akunza da ke yankin Ashige a karamar hukumar Lafia.

Ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnati na aiki kafada da kafada da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki wajen aiwatar da sabbin matakan tsaro domin shawo kan irin waɗannan hare-hare.

Ya kuma yi kira ga ’yan ƙasa da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen kama masu aikata laifuka a dukkan sassan jihar.

Mista Ahemba ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na yin duk mai yiwuwa domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Saboda haka, ya roki jama’a da su rika kai rahoton duk wani abu da suke zargin ba daidai ba ga hukumomin da suka dace, tare da ba da cikakken haɗin kai ga jami’an tsaro domin hana aikata laifuka da yaki da su.

COV: Aliyu Muraki / Lafia

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara