Connect with us

Ilimi

An Sace Ɗalibai 1,683 a Makarantu cikin Shekaru 8 – Rahoto

Published

on

Aƙalla yara da ɗalibai 1,683 ne aka sace a makarantu a Najeriya tsakanin shekarun 2014 zuwa 2022, sakamakon hare-haren da ƙungiyoyin ’yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya suka kai makarantu har sau 70 a cikin wannan lokaci.

Wani rahoto da ƙungiyar agaji ta ƙasa da ƙasa, Save the Children International (SCI), ta fitar domin bikin Ranar Ilimi ta Duniya ta 2026, ya kuma bayyana cewa ɗalibai 184 sun rasa rayukansu a yayin waɗannan hare-hare, yayin da gine-ginen makarantu 25 suka lalace.

Rahoton, wanda aka miƙa wa ’yan jarida a Jihar Katsina, ya nuna cewa rikicin ya fi muni a jihohin Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma, inda hare-haren makarantu, sace-sacen jama’a gaba ɗaya, da ƙauracewar al’umma ke ci gaba da yawaita. Wannan na hana ƙoƙarin gwamnati da abokan hulɗa na inganta ingancin ilimi samun nasara.

Rahoton ya gargaɗi cewa, “ba tare da tabbatar da tsaron makarantu da kuma samar da isasshen kuɗaɗen da za a zuba a ɓangaren ilimi ba, ƙwarewa da baiwar matasan Najeriyawaɗanda suka haura kashi 60 cikin 100 na yawan alummaza su ci gaba da kasancewa a takure.”

Haka kuma, rahoton ya yi kira da a aiwatar da Dokar Kare Tsaron gaba ɗaya, tare da ɗaukar tsauraran matakan tsaro don kare yara a wuraren koyonsu. Ya bayyana matasa a matsayin “ba shugabannin gobe kaɗai ba, har ma manyan ginshiƙan sauyi a yau.

Rahoton ya ƙara da cewa ƙungiyar na ci gaba da jajircewa wajen ƙarfafa fafutukar matasa domin ganin an aiwatar da Shirin Kare Makarantu, tallafawa ilimi a lokutan gaggawa, da bunƙasa basira da ƙwarewar matasa da rikice-rikice da ƙauracewa suka shafa.

Isma’il Adamu

Labarai

Ilimi14 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara