Connect with us

Ilimi

An Sace Ɗalibai 1,683 a Makarantu cikin Shekaru 8 – Rahoto

Published

on

Aƙalla yara da ɗalibai 1,683 ne aka sace a makarantu a Najeriya tsakanin shekarun 2014 zuwa 2022, sakamakon hare-haren da ƙungiyoyin ’yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya suka kai makarantu har sau 70 a cikin wannan lokaci.

Wani rahoto da ƙungiyar agaji ta ƙasa da ƙasa, Save the Children International (SCI), ta fitar domin bikin Ranar Ilimi ta Duniya ta 2026, ya kuma bayyana cewa ɗalibai 184 sun rasa rayukansu a yayin waɗannan hare-hare, yayin da gine-ginen makarantu 25 suka lalace.

Rahoton, wanda aka miƙa wa ’yan jarida a Jihar Katsina, ya nuna cewa rikicin ya fi muni a jihohin Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma, inda hare-haren makarantu, sace-sacen jama’a gaba ɗaya, da ƙauracewar al’umma ke ci gaba da yawaita. Wannan na hana ƙoƙarin gwamnati da abokan hulɗa na inganta ingancin ilimi samun nasara.

Rahoton ya gargaɗi cewa, “ba tare da tabbatar da tsaron makarantu da kuma samar da isasshen kuɗaɗen da za a zuba a ɓangaren ilimi ba, ƙwarewa da baiwar matasan Najeriyawaɗanda suka haura kashi 60 cikin 100 na yawan alummaza su ci gaba da kasancewa a takure.”

Haka kuma, rahoton ya yi kira da a aiwatar da Dokar Kare Tsaron gaba ɗaya, tare da ɗaukar tsauraran matakan tsaro don kare yara a wuraren koyonsu. Ya bayyana matasa a matsayin “ba shugabannin gobe kaɗai ba, har ma manyan ginshiƙan sauyi a yau.

Rahoton ya ƙara da cewa ƙungiyar na ci gaba da jajircewa wajen ƙarfafa fafutukar matasa domin ganin an aiwatar da Shirin Kare Makarantu, tallafawa ilimi a lokutan gaggawa, da bunƙasa basira da ƙwarewar matasa da rikice-rikice da ƙauracewa suka shafa.

Isma’il Adamu

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara