Labarai
An jikkata Yan jarida bakwai a wani hari a Gaza
Akalla ƴan jarida bakwai ne suka jikkata sakamakon hari ta sama da Isra’ila ta kai asibiti a tsakiyar Gaza.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kai wa cibiyar bayar da umarni ta masu ikirarin jihadi da ke harabar asibitin al-Aqsa hari, inda ɗaruruwan mutane ke fake wa.
Mutane huɗu sun rasa rayukansu, ciki har da wani mutum guda da Isra’ila ta bayyana a matsayin kwamandan mayakan Jihadi.
A wani sabon labarin kuma, sojin Isra’ilan sun baje kolin makaman da suka ce sojojinsu sun kama a wani samame da suka kai asibitin al-Shifa da ke birnin Gaza, bayan zargin mayakan Hamas da ɓuya a cibiyoyin lafiya.
Jami’an lafiya a Falasɗinu sun ce mutane tara ne suka rasa rayukansu a harin da Isra’ila ta kai a Bani Suhaila da ke makwabtaka da Khan younis.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana