Connect with us

Labarai

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Published

on

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi ta yanar gizo na jam’iyyar, biyo bayan sauya shekar Gwamna Dauda Lawal zuwa jam’iyyar.

Sakataren gwamnatin jihar Zamfara, Malam Abubakar Mohammad Nakwada, ne ya bayyana hakan yayin da yake duba yadda ake gudanar da rajistar a cibiyoyi shida da ke kananan hukumomin Gusau da Bungudu.

A wata sanarwa da Mai ba Sakataren Gwamnatin Jihar shawara kan harkokin yada labarai, Suleman Ahmad Tudu, ya fitar, an ce Malam Nakwada ya nuna gamsuwa da yadda magoya bayan gwamnan suka fito da yawa domin yin rajista a APC.

Ya ce wannan lamari alama ce da ke nuna goyon bayan jama’a ga matakin da gwamnan ya dauka na shiga jam’iyyar.

Sanarwar ta kara da cewa sabbin mambobi 60,987 ne suka yi rajista cikin kwanaki uku da sake bude shafin rajistar, baya ga 97,710 da suka riga sun yi rajista tun kafin sauya shekar gwamnan.

Hakan ya sa jimillar mambobin APC a jihar ta kai 158,697 zuwa karfe 7:30 na yammacin ranar 15 ga Maris.

Haka kuma, a matsakaici ana samun kusan mutane 20,329 na yin rajista a kowace rana, abin da jami’an jam’iyyar suka ce na nuna karuwar goyon bayan jama’a ga APC a matakin kasa.

Malam Nakwada ya bayyana fatan cewa jam’iyyar za ta cimma adadin mambobin da take bukata kafin ranar 25 ga Maris, idan aka ci gaba da samun irin wannan yawan masu rajista.

Yayin ziyararsa a Bungudu, Sakataren gwamnatin jihar ya kuma shirya wata ganawar kai tsaye ta yanar gizo tsakanin masu rajistar da Gwamna Dauda Lawal, wanda ke kasar Saudiyya domin gudanar da Umrah.

A cikin ganawar, gwamnan ya yaba wa magoya bayansa bisa juriyar da suka nuna da kuma yadda suka fito da yawa duk da tsananin zafi da kuma azumin watan Ramadan.

Ya kuma sake jaddada kudurin gwamnatinsa na ci gaba da aiki domin kare muradun al’ummar jihar Zamfara.

Sakataren gwamnatin ya samu rakiyar mai kula da rajistar a jihar, Hon. Naziru Ibrahim, da kuma Kwamishinan kananan hukumomi da harkokin sarauta, Injiniya Ahmad Garba Yandi, tare da sauran jami’ai.

Aminu Dalhatu/Gusau

Labarai

Labarai14 hours ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai18 hours ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai22 hours ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai23 hours ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai1 day ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai1 day ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai1 day ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai1 day ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai4 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai4 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara