Connect with us

Kasuwanci

Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano

Published

on

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa gobara ta lalata rumfuna 529 daga cikin rumfuna na wucin gadi a Kasuwar Shuwaki da ke ƙaramar hukumar Gari, Jihar Kano.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar, Alhaji Saminu Abdullahi, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Kano.

A cewarsa, hukumar ta samu kiran gaggawa misalin ƙarfe 3:25 na rana daga Abdulmalik Muhammad na ofishin kashe gobara na Gari, yana sanar da aukuwar gobara a kasuwar.

Ya bayyana cewa, da zarar sun samu bayanin, hukumar ta aika jami’ai da motocin kashe gobara zuwa wurin domin kashe wutar tare da hana ta yaduwa zuwa sauran sassan kasuwar.

Saminu ya ce yankin kasuwar yana da fadin kimanin kafa 3,000 da 2,500, kuma yana ɗauke da kusan rumfuna 1,000 na wucin gadi, inda rumfuna 529 suka ƙone ƙurmus.

Sai dai ya tabbatar cewa ba a rasa rai ba a wannan hatsari.

Ya danganta musabbabin gobarar da aikace-aikacen wasu mutane masu shaye-shaye da ke zaune a cikin kasuwar.

Mai magana da yawun hukumar ya shawarci jama’a da ’yan kasuwa da su kasance masu hankali da taka-tsantsan wajen amfani da wuta da abubuwan da ke iya kama da wuta, domin kauce wa irin wannan ibtila’i a nan gaba.

Khadijah Aliyu

 

Labarai

Labarai2 days ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai2 days ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai2 days ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai2 days ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai2 days ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai2 days ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai5 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai5 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara