Connect with us

Labarai

Limamin Pangu Gari Ya Nemi Gwamnan Neja Ya Sanya Baki Kan Rikicin Fili A Yankin

Published

on

An yi kira ga Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja da ya sanya baki kan rikicin fili mai fadin sama da hektar saba’in da biyar da ake zargin Hakimin Tegina da ke karamar hukumar Rafi ya kwace daga hannun mamallakinsa a Pangu Gari.

 

Babban Limamin Pangu Gari, Alhaji Umar Musa Danladi ne ya yi wannan kiran yayin da yake zantawa da manema labarai  a Minna, inda ya bayyana cewa hakan yana da muhimmanci matuka,  domin dakile  rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

 

Alhaji Umar Musa Danladi ya bayyana cewa ya gaji filin gonar ne daga mahaifinsa wanda ya rasu kusan shekaru goma da suka gabata, kuma yana da burin barin filin ga ‘ya’yansa su gada.

 

Babban Limamin ya bayyana cewa  wata kotun Shari’a da ke yankin  ta shiga tsakaninsa da wani mutum da ya gina shago a cikin filin, haka kuma ya ci nasara a wata kara da ke dauke da lamba SC/Teg/Cr_25/2024 da ya shigar kan  Hakimin Tegina da wasu mutum bakwai a bara.

 

A cewarsa, ci gaba da cin zarafin da Hakimin Tegina, Alhaji Garba Bako ke yi masa, wani abu ne da ke nuna raina kotu, wanda ya kamata a dauki mataki cikin gaggawa domin samar da zaman lafiya mai dorewa bisa ka’idojin adalci, da gaskiya da gudanar da aiki da nagarta da gwamnatin Gwamna Mohammed Umar Bago ke tsayawa a kai.

 

Sai dai ya zargi Hakimin Tegina, Alhaji Garba Bako, da cewa ya bayar da wani yanki na filin gonar nasa ga wasu manoma domin su noma, tare da umartar jami’an tsaro su kama Babban Limamin Pangu Gari da duk wani dan uwansa da aka gani a filin gonar.

 

Alhaji Musa Umar Danladi ya kuma nemi Sarkin Kagara, Alhaji Attahiru Gunna na biyu wanda ya bayyana a matsayin masoyin zaman lafiya, da ya kara shiga tsakani a rikicin filin gonar domin ya samun abin da ya ce mallakinsa ne na hakika.

 

Ya kuma bukaci ‘yan uwansa su ci gaba da kasancewa cikin zaman lafiya tare da jiran amsa mai kyau da shiga tsakani daga bakin Gwamnan Jihar Neja da kuma Sarkin Kagara, wadanda ya bayyana a matsayin mutane masu gaskiya da adalci akan aikinsu.

 

Daga Aliyu Lawa

 

 

Labarai

Labarai19 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara