Connect with us

Labarai

Sojojin Sudan Sun Kace Birnin El-Obeid Daga Hannun RSF

Published

on

Sojojin Sudan sun ce sun kawo ƙarshen iko da birnin el-Obeid na yankin kudancin ƙasar na kusan shekaru biyu da dakarun RSF suka yi.

Wannan nasara na zuwa ne ‘ƴan sa’o’i bayan da RSF ta rattaɓa hannu kan yarjejeniyar siyasa a Nairobi da ke ƙasar Kenya na kafa gwamnatin aware a yankunan da ke ƙarƙshin ikonta.

Tun dai shekarar 2023 ne rundunar RSF da sojojin Sudan ke fafatawa, inda dubban fararen hula ke mutuwa sannan da dama na barin gidajensu.

Rikicin dai ya raba ƙasar ɓangarori biyu, inda sojoji ke iko da arewa da gabashi, yayin da su kuma RSF ke iko da mafi yawancin yankin Darfur da ke yammaci da wasu sassan kudanci.

Birnin El-Obaid dai wanda shi ne babban birnin jihar Kordofan, yana da matuƙar muhimmanci ga Khartoum, babban birnin ƙasar. Wannan ne wani yunƙuri na sojoji a ƴan makonnin nan tun bayan kame yankuna da dama na Khartoum daga hannun RSF.

Al’ummar Sudan sun fito tituna suna ta bayyana farin cikinsu dangane da sake ƙwato birnin daga hannun waɗanda suke bayyanawa a matsayin ƴan tawaye.

Wata mai fafutuka ƴar ƙasar Sudan, Dallia Abdlemoniem ta shaida wa BBC cewa ƙwace iko da birnin daga hannun RSF “gagarumar” nasara ce.

Ta ƙara da cewa sojoji na ci gaba da shirin kutsawa yammaci inda a can ne mayaƙan na RSF suke.

Dukkannin ɓangarorin biyu na sojojin gwamnati da na rundunar mayaƙan RSF sun musanta zarge-zargen take haƙƙin bil’ada da aka yi musu, da har ta kai Amurka ta ƙaƙaba wa jagororinsu takunkumai. Bugu da ƙari, an zargi RSF da aikata laifukan kisan ƙare dangi a Darfur.

An soki ƙasar Kenya bisa karɓar ɓakuncin da ta yi makon da ya wuce da ke son kafa gwamnatin ƴan aware.

Da ma dai gwamnatin sojin Sudan ta gargaɗi Kenya da cewa za ta yi ramuwar gayya kan Kenyar bisa matakin, kuma tuni ta yi wa jakadanta da ke Nairobi kiranye.

Sai dai a wani martani da suka yi, ministan harkokin wajen Kenya ya ce babu “wata mummunar manufa” a “bai wa dukkan ɓangarorin da ke rikici da juna dama.

bbc

Labarai

Labarai20 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara