Connect with us

Labarai

Gwamnatin Borno Ta Samar Da Gidaje Sama Da 400 Ga ‘Yan Gudun Hijira A Dalori

Published

on

Gwamnatin Jihar Borno ta fara rabon gidaje 447 na sake tsugunar da ‘yan gudun hijira a yankin Dalori dake karamar hukumar Konduga a jihar.

 

Gwamna Babagana Zulum wanda ya kaddamar da atisayen, ya kuma raba kayan abinci da sauran kayayyakin masarufi ga iyalan da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu.

 

Ya ce an zabo wadanda suka ci gajiyar tallafin ne daga sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kawar Maila, inda iyalai 197 suka sami gidaje, yayin da iyalai 250 daga sansanin Dalori suka amfana.

Ya ce an samar wa al’ummar da aka sake tsugunar da su asibiti da makaranta da  ruwan sha.

 

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa gwamnatinsa za ta kuma samar da kayayyakin noma da  tallafa ga ‘yan kasuwa domin ‘yan gudun hijirar da suka dawo su samu saukin ababen more rayuwa.

 

“Kowanne daga cikin gidajen 447, wadanda  suka kunshi mutane kusan dubu biyu da dari biyar  sun sami kayan abinci, da  tabarmi, da barguna da tufafi.” In ji Gwamna Zulum.

 

Zulum ya kuma yi tsokaci kan shirin sake ginawa da kuma tsugunar da al’ummar Dalwa da Sandiya da ‘yan ta’addan Boko Haram suka raba da muhallansu a karamar hukumar Konduga.

 

Hakazalika, Gwamna Babagana Zulum ya kuma bayar da umarnin rufe dukkan sansanonin ‘yan gudun hijira da ba  hukuma  ta kafa su ba  a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

 

Ya ce ba za a ci gaba da ajiye mutane a sansanoni ba, yana mai jaddada cewa za a rufe dukkan sansanoni da ke Maiduguri kafin ranar 29 ga Mayun 2024.

 

“Muna so a sami kamulallun  mutane  a cikin al’ummoma daban-daban domin bayar da gudummawar ci gaban jihar, don haka za mu mayar da su gidajensu domin su ci gaba da gudanar da al’amuran su na yau da kullun”. Inji  shi.

 

Gwamnan ya bayyana cewa an rufe dukkanin sansanonin ‘yan gudun hijira da gwamnati ta kafa a birnin Maiduguri da kewaye tun shekarar da ta gabata.

 

Daga Dauda Iliya

1 Comment

1 Comment

  1. Haladu Abdullahi

    February 28, 2024 at 5:50 am

    MUNA YABAWA GOMNA BABAGANA BISA WANNAN GAGARUMI AIKI DA YAYI

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai5 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara