Connect with us

Ilimi

Shugaba Tinubu Ya Jaddada Kudurin Gwamnatinsa Na Ƙara Zuba Jari A Ilimi

Published

on

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ƙara zuba jari a manyan cibiyoyin ilimi domin shirya ɗalibai su zama masu iya fafatawa a matakin duniya.

Shugaban Ƙasan ya bayyana hakan ne a yayin bikin karrama masu kammala karatu na shekara ta 40 na Jami’ar Ilorin (UNILORIN) da ke Ilorin, Jihar Kwara.

A jawabinsa, wanda Shugaban Jami’ar Fasaha ta Tarayya Akure (FUTA), Farfesa Temidayo Oladiji, ya karanta a madadinsa, Shugaba Tinubu ya yi alkawarin ƙarfafa ƙirƙira, bincike, da ilimin da ke gina ƙwarewa (skill-based education) a dukkan jami’o’in Najeriya.

Ya yaba wa jami’ar bisa tsayin daka da ladabi da kuma ingancin ilimi da ta dade tana nunawa tun daga kafuwarta.

Shugaban Ƙasan ya kuma sanar da cewa Jami’ar Ilorin ta kasance ɗaya daga cikin jami’o’in da aka zaɓa domin zama hedikwatar “Digital Innovation Hub” na Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) — wani shiri da aka ƙaddamar domin bunƙasa ƙwarewar fasaha, ƙirƙira, da haɓaka bincike a jami’o’i.

A nasa jawabin, Shugaban Jami’ar Ilorin, Farfesa Wahab Egbewole, ya shawarci waɗanda suka kammala karatu da su ci gaba da riƙe dabi’un jami’ar na ladabi, aiki tukuru, da gaskiya, domin su zama abin koyi a inda suka samu kansu a gaba.

Ali Muhammad Rabiu

 

Labarai

Ilimi14 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara