Connect with us

Labarai

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

Published

on

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin arziki da al’adun ƙasar nan.

Tsohon Daraktan gudanarwa na Radio Nigeria Kaduna kuma gogaggen ɗan jarida, Alhaji Halilu Ahmad Getso, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da wakilin Radio Nigeria a Kano, a wani ɓangare na bikin cika shekaru 75 da kafuwar gidan rediyon.

Getso ya ce asalin kafuwar wannan hukuma ya samo tushe ne tun zamanin Nigerian Broadcasting Corporation (NBC), wadda aka kafa a lokacin marigayi Firimiya na Arewacin Najeriya, Ahmadu Bello.

Ya bayyana cewa a farkon shekarun, an kafa ƙananan tashoshi ne kawai a Kano da Maiduguri, waɗanda ake haɗawa da Kaduna domin watsa shirye-shirye da kuma daidaita ayyukan rediyo.

A cewarsa, gidan rediyon ya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa rayuwar al’umma ta hanyar shirye-shirye masu tasiri da suka mayar da hankali kan bukatun jama’a, ilimi da kuma kyawawan ɗabi’u.

Gogaggen ɗan jaridar ya kuma tuna da yadda hukumomin tsohuwar gwamnatin yankin Arewa suka sayo rediyo tare da rarraba su ga al’ummomin karkara domin ƙara musu damar samun bayanai da sadarwa.

Ya ƙara da cewa a wancan lokaci, shahararrun shirye-shirye sun haɗa da karatun Alƙur’ani da kuma shirye-shiryen da suka shafi ci gaban al’umma, waɗanda suka ja hankalin masu sauraro da dama.

Getso ya kuma bayyana cewa yawancin ma’aikatan Hukumar Rediyon Tarayya ta Najeriya (FRCN) a yanzu, sun fara aiki ne tun a NBC, abin da ke nuna ci gaba da gogewa a cikin tsarin aikin.

Ya ce kamfanin watsa shirye-shirye na Arewacin Najeriya, wanda shi ma aka kafa a ƙarƙashin jagorancin Ahmadu Bello, daga bisani ya rikide zuwa Radio Nigeria Kaduna, lamarin da ya ƙarfafa harkar watsa shirye-shirye a yankin.

Yayin da yake yaba gudunmawar da gidan rediyon ya bayar tsawon shekaru, Getso ya buƙaci ma’aikata su ƙara ƙaimi wajen inganta ayyukan su domin su dace da sabbin ƙa’idojin aikin watsa shirye-shirye na zamani.

Haka kuma, ya yi addu’ar fatan alheri ga ci gaba da ɗaukakar Radio Nigeria da sauran tashoshin FRCN a faɗin ƙasar.

Abdullahi Jalaluddeen, Kano

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara