Connect with us

Labarai

Masu Tasiri a Kafafen Sada Zumunta sun samu horo kan RMNCAH+N, Tsarin Iyali da Rigakafin Cin Zarafin Mata

Published

on

Ƙungiyar Centre for Communication and Social Impact (CCSI) tare da haɗin gwiwar abokan aikin ta na EngenderHealth Consortium sun shirya taron horo na yini ɗaya a Kano domin ƙarfafa ƙwarewar ’yan jarida da masu tasiri a kafafen sada zumunta (social media influencers) wajen yada sahihan bayanai da tallafawa manufofin kiwon lafiya da daidaito tsakanin jinsi.

 

Taron, mai taken “Daga Masu Bi zuwa Masu Faɗa Aji: Amfani da Kafafen Sada Zumunta wajen Yaɗa Sawun Lafiya da Daidaito”, ya mayar da hankali ne kan batutuwan Reproductive, Maternal, Newborn, Child, and Adolescent Health plus Nutrition (RMNCAH+N), Family Planning (FP), da Gender, Youth, and Social Inclusion (GYSI).

 

Manufar wannan horo ita ce canza masu tasiri a kafafen sada zumunta zuwa ƙwararrun masu fafutukar yaɗa ilimin lafiya da canjin halayyar jama’a ta hanyar amfani da hujjoji, ladabi, da al’adun da suka dace da al’umma.

 

A jawabinsa na budewa, Atiku Muhammad Auwal, Manajan Ayyukan Wayar da Kai na CCSI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce samar wa masu tasiri a kafafen sada zumunta da ilimi da dabaru domin su zama masu faɗakarwa kan batutuwan RMNCAH+N, Tsarin Iyali, da Daidaito tsakanin jinsi.

 

Ya ce, horon zai taimaka musu wajen jan hankalin gwamnati da al’umma kan muhimman batutuwan lafiyar jama’a ta hanyar ingantacciyar fafutuka.

 

“Ta hanyar koyarwa daga masana da atisayen aiki, mahalarta sun koyi dabarun ƙirƙirar abun ciki na dijital mai tasiri, gaskiya, da tausayi ga waɗanda abin ya shafa, tare da hanyoyin yaki da labaran ƙarya da ƙarfafa tattaunawa mai haɗin kai,” in ji shi.

 

A cikin gabatarwarta mai taken “Matsayin RMNCAH+N, FP da GBV a Jihar Kano da rawar da masu tasiri ke takawa wajen kawo sauyi”, Dr. Mansurah, mai kula da shirye-shiryen Maternal, Newborn and Child Health (MNCH) a jihar, ta bayyana manyan ƙalubale da ke fuskantar sashen lafiya a Kano.

 

Ta ambaci matsalolin kamar rashin daidaiton rarraba cibiyoyin lafiya (PHCs), ƙarancin ƙwararrun ma’aikatan haihuwa, gibin kayan aiki da gini, ƙarancin kayan lafiya, ƙarancin kwarin gwiwar ma’aikata, raunin tsarin bayanai, da kuma rashin haɗin kan al’umma.

 

Shi kuwa Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Kano, Kwamared Mustapha Gambo Muhammad, ya jaddada cewa NUJ na gaba-gaba wajen yaƙi da cin zarafin mata da inganta ilimin lafiya, tsare iyali, da daidaito tsakanin jinsi.

 

Ya tabbatar da kudirin ƙungiyar wajen ci gaba da wayar da kai ta hanyar kafafen sada zumunta da rahotanni masu inganci.

 

A nata jawabin, Khadijah Abdullahi Yahaya daga Arewa Radio, ta jaddada rawar da masu tasiri da kafafen watsa labarai ke takawa wajen tallafawa shirye-shiryen tsare iyali da RMNCAH+N.

 

Ta yi kira da a ƙara haɗin kai da bayar da dama ga jama’a su rika bayyana irin ƙalubalen da suke fuskanta a cikin al’ummarsu.

 

Taron ya ƙunshi gabatarwa masu mu’amala, tambayoyi da amsoshi tare da masana lafiya, da damar haɗa kai tsakanin masu tasiri, ’yan jarida, da masu ruwa da tsaki a harkokin lafiya.

 

Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara