Labarai
Masu Tasiri a Kafafen Sada Zumunta sun samu horo kan RMNCAH+N, Tsarin Iyali da Rigakafin Cin Zarafin Mata
Ƙungiyar Centre for Communication and Social Impact (CCSI) tare da haɗin gwiwar abokan aikin ta na EngenderHealth Consortium sun shirya taron horo na yini ɗaya a Kano domin ƙarfafa ƙwarewar ’yan jarida da masu tasiri a kafafen sada zumunta (social media influencers) wajen yada sahihan bayanai da tallafawa manufofin kiwon lafiya da daidaito tsakanin jinsi.
Taron, mai taken “Daga Masu Bi zuwa Masu Faɗa Aji: Amfani da Kafafen Sada Zumunta wajen Yaɗa Sawun Lafiya da Daidaito”, ya mayar da hankali ne kan batutuwan Reproductive, Maternal, Newborn, Child, and Adolescent Health plus Nutrition (RMNCAH+N), Family Planning (FP), da Gender, Youth, and Social Inclusion (GYSI).
Manufar wannan horo ita ce canza masu tasiri a kafafen sada zumunta zuwa ƙwararrun masu fafutukar yaɗa ilimin lafiya da canjin halayyar jama’a ta hanyar amfani da hujjoji, ladabi, da al’adun da suka dace da al’umma.
A jawabinsa na budewa, Atiku Muhammad Auwal, Manajan Ayyukan Wayar da Kai na CCSI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce samar wa masu tasiri a kafafen sada zumunta da ilimi da dabaru domin su zama masu faɗakarwa kan batutuwan RMNCAH+N, Tsarin Iyali, da Daidaito tsakanin jinsi.
Ya ce, horon zai taimaka musu wajen jan hankalin gwamnati da al’umma kan muhimman batutuwan lafiyar jama’a ta hanyar ingantacciyar fafutuka.
“Ta hanyar koyarwa daga masana da atisayen aiki, mahalarta sun koyi dabarun ƙirƙirar abun ciki na dijital mai tasiri, gaskiya, da tausayi ga waɗanda abin ya shafa, tare da hanyoyin yaki da labaran ƙarya da ƙarfafa tattaunawa mai haɗin kai,” in ji shi.
A cikin gabatarwarta mai taken “Matsayin RMNCAH+N, FP da GBV a Jihar Kano da rawar da masu tasiri ke takawa wajen kawo sauyi”, Dr. Mansurah, mai kula da shirye-shiryen Maternal, Newborn and Child Health (MNCH) a jihar, ta bayyana manyan ƙalubale da ke fuskantar sashen lafiya a Kano.
Ta ambaci matsalolin kamar rashin daidaiton rarraba cibiyoyin lafiya (PHCs), ƙarancin ƙwararrun ma’aikatan haihuwa, gibin kayan aiki da gini, ƙarancin kayan lafiya, ƙarancin kwarin gwiwar ma’aikata, raunin tsarin bayanai, da kuma rashin haɗin kan al’umma.
Shi kuwa Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Kano, Kwamared Mustapha Gambo Muhammad, ya jaddada cewa NUJ na gaba-gaba wajen yaƙi da cin zarafin mata da inganta ilimin lafiya, tsare iyali, da daidaito tsakanin jinsi.
Ya tabbatar da kudirin ƙungiyar wajen ci gaba da wayar da kai ta hanyar kafafen sada zumunta da rahotanni masu inganci.
A nata jawabin, Khadijah Abdullahi Yahaya daga Arewa Radio, ta jaddada rawar da masu tasiri da kafafen watsa labarai ke takawa wajen tallafawa shirye-shiryen tsare iyali da RMNCAH+N.
Ta yi kira da a ƙara haɗin kai da bayar da dama ga jama’a su rika bayyana irin ƙalubalen da suke fuskanta a cikin al’ummarsu.
Taron ya ƙunshi gabatarwa masu mu’amala, tambayoyi da amsoshi tare da masana lafiya, da damar haɗa kai tsakanin masu tasiri, ’yan jarida, da masu ruwa da tsaki a harkokin lafiya.
Khadijah Aliyu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
