Connect with us

Labarai

Masu Tasiri a Kafafen Sada Zumunta sun samu horo kan RMNCAH+N, Tsarin Iyali da Rigakafin Cin Zarafin Mata

Published

on

Ƙungiyar Centre for Communication and Social Impact (CCSI) tare da haɗin gwiwar abokan aikin ta na EngenderHealth Consortium sun shirya taron horo na yini ɗaya a Kano domin ƙarfafa ƙwarewar ’yan jarida da masu tasiri a kafafen sada zumunta (social media influencers) wajen yada sahihan bayanai da tallafawa manufofin kiwon lafiya da daidaito tsakanin jinsi.

 

Taron, mai taken “Daga Masu Bi zuwa Masu Faɗa Aji: Amfani da Kafafen Sada Zumunta wajen Yaɗa Sawun Lafiya da Daidaito”, ya mayar da hankali ne kan batutuwan Reproductive, Maternal, Newborn, Child, and Adolescent Health plus Nutrition (RMNCAH+N), Family Planning (FP), da Gender, Youth, and Social Inclusion (GYSI).

 

Manufar wannan horo ita ce canza masu tasiri a kafafen sada zumunta zuwa ƙwararrun masu fafutukar yaɗa ilimin lafiya da canjin halayyar jama’a ta hanyar amfani da hujjoji, ladabi, da al’adun da suka dace da al’umma.

 

A jawabinsa na budewa, Atiku Muhammad Auwal, Manajan Ayyukan Wayar da Kai na CCSI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce samar wa masu tasiri a kafafen sada zumunta da ilimi da dabaru domin su zama masu faɗakarwa kan batutuwan RMNCAH+N, Tsarin Iyali, da Daidaito tsakanin jinsi.

 

Ya ce, horon zai taimaka musu wajen jan hankalin gwamnati da al’umma kan muhimman batutuwan lafiyar jama’a ta hanyar ingantacciyar fafutuka.

 

“Ta hanyar koyarwa daga masana da atisayen aiki, mahalarta sun koyi dabarun ƙirƙirar abun ciki na dijital mai tasiri, gaskiya, da tausayi ga waɗanda abin ya shafa, tare da hanyoyin yaki da labaran ƙarya da ƙarfafa tattaunawa mai haɗin kai,” in ji shi.

 

A cikin gabatarwarta mai taken “Matsayin RMNCAH+N, FP da GBV a Jihar Kano da rawar da masu tasiri ke takawa wajen kawo sauyi”, Dr. Mansurah, mai kula da shirye-shiryen Maternal, Newborn and Child Health (MNCH) a jihar, ta bayyana manyan ƙalubale da ke fuskantar sashen lafiya a Kano.

 

Ta ambaci matsalolin kamar rashin daidaiton rarraba cibiyoyin lafiya (PHCs), ƙarancin ƙwararrun ma’aikatan haihuwa, gibin kayan aiki da gini, ƙarancin kayan lafiya, ƙarancin kwarin gwiwar ma’aikata, raunin tsarin bayanai, da kuma rashin haɗin kan al’umma.

 

Shi kuwa Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Kano, Kwamared Mustapha Gambo Muhammad, ya jaddada cewa NUJ na gaba-gaba wajen yaƙi da cin zarafin mata da inganta ilimin lafiya, tsare iyali, da daidaito tsakanin jinsi.

 

Ya tabbatar da kudirin ƙungiyar wajen ci gaba da wayar da kai ta hanyar kafafen sada zumunta da rahotanni masu inganci.

 

A nata jawabin, Khadijah Abdullahi Yahaya daga Arewa Radio, ta jaddada rawar da masu tasiri da kafafen watsa labarai ke takawa wajen tallafawa shirye-shiryen tsare iyali da RMNCAH+N.

 

Ta yi kira da a ƙara haɗin kai da bayar da dama ga jama’a su rika bayyana irin ƙalubalen da suke fuskanta a cikin al’ummarsu.

 

Taron ya ƙunshi gabatarwa masu mu’amala, tambayoyi da amsoshi tare da masana lafiya, da damar haɗa kai tsakanin masu tasiri, ’yan jarida, da masu ruwa da tsaki a harkokin lafiya.

 

Khadijah Aliyu

Labarai

Ilimi14 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara