Connect with us

Kasuwanci

Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro

Published

on

Majalisar Tattalin Arzikin Ƙasa (NEC) ta amince da shirin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu na sake fasalin da kuma zamanantar da cibiyoyin horar da jami’an tsaro a faɗin ƙasar. Wannan mataki ya biyo bayan taron majalisar na 152 da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda Ministan Tsare-tsaren Kasafi da Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya gabatar da jawabi kan dabarun cimma burin Shugaban Ƙasa na samar da tattalin arzikin da ya kai darajar dala tiriliyan guda.

An kafa kwamitin da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ke jagoranta don tsara cikakken tsari na gyaran da sabunta cibiyoyin horar da jami’an ƴan sanda da sauran hukumomin tsaro cikin wata guda. Mambobin kwamitin sun haɗa da gwamnonin jihohin Kaduna, Ogun, Taraba, Akwa Ibom, Zamfara, da Nasarawa, yayin da tsohon Sufeton ƴan sanda na ƙasa, Baba Usman, zai zama sakataren kwamitin.

Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin inganta yanayin cibiyoyin horar da jami’an tsaro domin ƙara ƙarfin horo da ƙwarewa tare da tabbatar da ƙwararru da ƙwarin gwiwar ma’aikatan tsaro.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, wanda ya jagoranci taron, ya shawarci gwamnatocin jihohi su mai da hankali wajen inganta rayuwar jama’a ta hanyar gwamnati mai ma’ana da shiri na gaba. Haka kuma, majalisar ta duba bayanin da Ofishin Mai Ba da Shawara Kan Tsaron Ƙasa (ONSA) ya gabatar kan tsarin tunkarar matsalar ambaliyar ruwa, wanda ke da nufin ƙarfafa tsarin gargadin gaggawa da shirin kare jama’a daga ambaliyar ruwa a ƙasar baki ɗaya.

Dangane da burin tattalin arzikin gwamnati, Sanata Bagudu ya gabatar da taswirar cimma tattalin arzikin dala tiriliyan guda nan da shekarar 2033, wanda ke ta’allaka da daidaiton tattalin arziki, samar da ayyukan yi, wadatar abinci da inganta gasa tsakanin jihohi.

NEC ta kuma yaba da tsarin cimma Muradin aikin gona na jihar Katsina tare da shawartar sauran jihohi su rungumi irin wannan tsarin na fasaha domin ƙara yawan amfanin gona da haɗa manoma da tsarin gwamnati. Majalisar ta kuma umarci Ma’aikatar Noma da samarda Abinci ta haɗa da kafa cibiyoyin bayanai da lura da harkokin noma a kowace yankin siyasa a kasafin 2026.

Kwamitin NEC na wucin gadi kan satar man fetur, ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya bayyana cigaba da aka samu wajen haɗa kai da manyan masu ruwa da tsaki a masana’antar mai don dakile satar man. Majalisar ta ƙarfafa kwamitin da ya ƙara zage damtse wajen ƙara yawan fitar da danyen mai sama da ganga miliyan 1.72 a kowace rana tare da faɗaɗa aikin sa zuwa kan satar ma’adinai. Ana sa ran Najeriya za ta kai matakin samar da ganga miliyan 2.5 na danyen mai a kowace rana nan da ƙarshen shekarar 2025.

Bello Wakili

 

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara