Connect with us

Kasuwanci

Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro

Published

on

Majalisar Tattalin Arzikin Ƙasa (NEC) ta amince da shirin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu na sake fasalin da kuma zamanantar da cibiyoyin horar da jami’an tsaro a faɗin ƙasar. Wannan mataki ya biyo bayan taron majalisar na 152 da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda Ministan Tsare-tsaren Kasafi da Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya gabatar da jawabi kan dabarun cimma burin Shugaban Ƙasa na samar da tattalin arzikin da ya kai darajar dala tiriliyan guda.

An kafa kwamitin da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ke jagoranta don tsara cikakken tsari na gyaran da sabunta cibiyoyin horar da jami’an ƴan sanda da sauran hukumomin tsaro cikin wata guda. Mambobin kwamitin sun haɗa da gwamnonin jihohin Kaduna, Ogun, Taraba, Akwa Ibom, Zamfara, da Nasarawa, yayin da tsohon Sufeton ƴan sanda na ƙasa, Baba Usman, zai zama sakataren kwamitin.

Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin inganta yanayin cibiyoyin horar da jami’an tsaro domin ƙara ƙarfin horo da ƙwarewa tare da tabbatar da ƙwararru da ƙwarin gwiwar ma’aikatan tsaro.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, wanda ya jagoranci taron, ya shawarci gwamnatocin jihohi su mai da hankali wajen inganta rayuwar jama’a ta hanyar gwamnati mai ma’ana da shiri na gaba. Haka kuma, majalisar ta duba bayanin da Ofishin Mai Ba da Shawara Kan Tsaron Ƙasa (ONSA) ya gabatar kan tsarin tunkarar matsalar ambaliyar ruwa, wanda ke da nufin ƙarfafa tsarin gargadin gaggawa da shirin kare jama’a daga ambaliyar ruwa a ƙasar baki ɗaya.

Dangane da burin tattalin arzikin gwamnati, Sanata Bagudu ya gabatar da taswirar cimma tattalin arzikin dala tiriliyan guda nan da shekarar 2033, wanda ke ta’allaka da daidaiton tattalin arziki, samar da ayyukan yi, wadatar abinci da inganta gasa tsakanin jihohi.

NEC ta kuma yaba da tsarin cimma Muradin aikin gona na jihar Katsina tare da shawartar sauran jihohi su rungumi irin wannan tsarin na fasaha domin ƙara yawan amfanin gona da haɗa manoma da tsarin gwamnati. Majalisar ta kuma umarci Ma’aikatar Noma da samarda Abinci ta haɗa da kafa cibiyoyin bayanai da lura da harkokin noma a kowace yankin siyasa a kasafin 2026.

Kwamitin NEC na wucin gadi kan satar man fetur, ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya bayyana cigaba da aka samu wajen haɗa kai da manyan masu ruwa da tsaki a masana’antar mai don dakile satar man. Majalisar ta ƙarfafa kwamitin da ya ƙara zage damtse wajen ƙara yawan fitar da danyen mai sama da ganga miliyan 1.72 a kowace rana tare da faɗaɗa aikin sa zuwa kan satar ma’adinai. Ana sa ran Najeriya za ta kai matakin samar da ganga miliyan 2.5 na danyen mai a kowace rana nan da ƙarshen shekarar 2025.

Bello Wakili

 

 

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara