Kasuwanci
Cutar Sankarau Ta Kashe Mutane 56 A Kebbi
Gwamnatin jihar Kebbi, ta tabbatar da mutuwar mutane 56 a sakamakon barkewar cutar sankarau a jihar inda 25 a Gwandu, 16 a Jega, 14 kuma suka mutu a kananan hukumomin Aliero na jihar.
Da yake zantawa da manema labarai, babban sakatare a ma’aikatar lafiya ta jihar, Dakta Nuhu Koko, ya ce an samu jimillar mutane 653 da ake zargin sun kamu da cutar a kananan hukumomi biyar da suka hada da Aliero, Jega, Gwandu, Birnin Kebbi da Bunza.
A cewarsa, samfurorin da aka aiko da kuma tabbatarwa daga cibiyar bincike, yanzu jihar ta san yadda take magance cututtukan sankarau.
Ya kara da cewa, an aika samfurori 17 zuwa dakin gwaje-gwaje na kasa da kasa da ke Abuja domin tabbatar da su, 5 daga cikinsu sun dawo ba tare da wata matsala ba,5 kuma ba sun tabbatar da cutar ce yayin da Aliero aka samu bullar cutar guda 3, Gwandu 1 da Jega 1.
Dokta Koko ya ce, dukkan majinyatan guda biyar da suka kamu da cutar an yi musu magani kuma an sallame su, yayin da ake jiran sakamakon gwaji guda 7 a NRL Abuja.
Babban Sakatare, ya bayyana cewa, an samu allurai 3,000 na rigakafin CSM daga ma’aikatar lafiya da jin dadin jama’a ta tarayya kuma an rarraba su a fadin kananan hukumomi 3 masu fama da wannan cutar.
Ya bayyana cewa, an samar da cibiyoyin keɓewa tare da haɗin gwiwar MS a Gwandu, Jega da Aliero tare da katifu, magunguna da sauran kayan masarufi da aka samar wa ƙananan hukumomin da abin ya shafa.
COV/Abdullahi Tukur
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
