Connect with us

Fasaha

AGILE Kano Ta Tattauna da Malamai da Limamai Don Ƙarfafa Goyon Bayan Ilimin ’Yan Mata

Published

on

Shirin karfafa ilimin ‘ya’ya mata a jihar Kano ya shirya taron tattaunawa da malamai da limaman masallatan Juma’a domin ƙarfafa haɗin gwiwa da shugabannin addini wajen inganta goyon bayan al’umma ga ilimin ’yan mata a fadin jihar.

Taron, wanda yake ɗaya daga cikin dabarun haɗin kai na masu ruwa da tsaki na AGILE, yana da nufin ƙara samun damar karatu, tsayawa da kuma kammala karatun ’yan mata ta hanyar daidaita ayyukan shirin da dabi’u da imanin al’umma.

A jawabinsa, Shugaban Shirin AGILE na Jihar Kano, Malam Mujtapha Aminu, ya bayyana cewa an shirya taron ne domin fayyace wasu rashin fahimta da ake da su game da shirin, da kuma tabbatar da fahimtar juna tsakanin shugabannin addini.

A cewarsa, “Shigar malamai da limaman masallatan Juma’a cikin wannan shiri yana da matuƙar muhimmanci domin suna da tasiri wajen gina ra’ayin jama’a. Mun gayyace su ne domin mu wayar da kan su game da manufofi, sassa, da matakan aikin shirin AGILE.”

Malam Mujtapha ya ƙara bayyana cewa shirin ya riga ya haɗa kai da shugabannin gargajiya da na addini wajen duba kundin horarwa don tabbatar da cewa yana tafiya da koyarwar addinin Musulunci da kuma dabi’un Hausawa.

Ya roƙi dukkan masu ruwa da tsaki da su ci gaba da ba da goyon baya ga shirin tare da neman bayani a duk lokacin da wani abu ya taso, domin kauce wa rashin fahimta. Ya jaddada cewa, “Malamai sune manyan masu tasiri wajen bunƙasa ilimin ’yan mata a Kano da Najeriya gaba ɗaya.”

A sakon sa na fatan alheri, Shugaban Majalisar Malamai ta Jihar Kano, Sheikh Ibrahim Khalil, wanda Sakatarensa Sheikh Ibrahim Abubakar Tofa ya wakilta, ya shawarci tawagar AGILE da su tabbatar dukkan sassan shirin suna tafiya da ka’idojin Musulunci da al’adun mutanen Kano, domin jihar na da tsarin rayuwa mai zurfi da al’adu masu ƙarfi.

Ya ce, “A matsayarmu na manyan masu ruwa da tsaki, muna da muhimmiyar rawa wajen tallafa wa ilimin ’yan mata domin Musulunci yana ƙarfafa neman ilimi ga maza da mata duka.”

Haka kuma, ya yi kira ga masu gudanar da shirin da su ci gaba da haɗa kai da dukkan masu ruwa da tsaki don gujewa yaɗuwar bayanan ƙarya da kuma tabbatar da gaskiya a duk matakan aiwatarwa.

Taron ya ƙunshi gabatar da cikakkun bayanai kan manyan sassan uku na shirin AGILE, tattaunawa tsakanin mahalarta, da zaman tambayoyi da amsoshi inda malamai suka gabatar da tambayoyi kan wasu bangarorin shirin kuma aka basu bayanai dalla-dalla.

Khadijah Aliyu

Labarai

Ilimi14 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara