Connect with us

Fasaha

AGILE Kano Ta Tattauna da Malamai da Limamai Don Ƙarfafa Goyon Bayan Ilimin ’Yan Mata

Published

on

Shirin karfafa ilimin ‘ya’ya mata a jihar Kano ya shirya taron tattaunawa da malamai da limaman masallatan Juma’a domin ƙarfafa haɗin gwiwa da shugabannin addini wajen inganta goyon bayan al’umma ga ilimin ’yan mata a fadin jihar.

Taron, wanda yake ɗaya daga cikin dabarun haɗin kai na masu ruwa da tsaki na AGILE, yana da nufin ƙara samun damar karatu, tsayawa da kuma kammala karatun ’yan mata ta hanyar daidaita ayyukan shirin da dabi’u da imanin al’umma.

A jawabinsa, Shugaban Shirin AGILE na Jihar Kano, Malam Mujtapha Aminu, ya bayyana cewa an shirya taron ne domin fayyace wasu rashin fahimta da ake da su game da shirin, da kuma tabbatar da fahimtar juna tsakanin shugabannin addini.

A cewarsa, “Shigar malamai da limaman masallatan Juma’a cikin wannan shiri yana da matuƙar muhimmanci domin suna da tasiri wajen gina ra’ayin jama’a. Mun gayyace su ne domin mu wayar da kan su game da manufofi, sassa, da matakan aikin shirin AGILE.”

Malam Mujtapha ya ƙara bayyana cewa shirin ya riga ya haɗa kai da shugabannin gargajiya da na addini wajen duba kundin horarwa don tabbatar da cewa yana tafiya da koyarwar addinin Musulunci da kuma dabi’un Hausawa.

Ya roƙi dukkan masu ruwa da tsaki da su ci gaba da ba da goyon baya ga shirin tare da neman bayani a duk lokacin da wani abu ya taso, domin kauce wa rashin fahimta. Ya jaddada cewa, “Malamai sune manyan masu tasiri wajen bunƙasa ilimin ’yan mata a Kano da Najeriya gaba ɗaya.”

A sakon sa na fatan alheri, Shugaban Majalisar Malamai ta Jihar Kano, Sheikh Ibrahim Khalil, wanda Sakatarensa Sheikh Ibrahim Abubakar Tofa ya wakilta, ya shawarci tawagar AGILE da su tabbatar dukkan sassan shirin suna tafiya da ka’idojin Musulunci da al’adun mutanen Kano, domin jihar na da tsarin rayuwa mai zurfi da al’adu masu ƙarfi.

Ya ce, “A matsayarmu na manyan masu ruwa da tsaki, muna da muhimmiyar rawa wajen tallafa wa ilimin ’yan mata domin Musulunci yana ƙarfafa neman ilimi ga maza da mata duka.”

Haka kuma, ya yi kira ga masu gudanar da shirin da su ci gaba da haɗa kai da dukkan masu ruwa da tsaki don gujewa yaɗuwar bayanan ƙarya da kuma tabbatar da gaskiya a duk matakan aiwatarwa.

Taron ya ƙunshi gabatar da cikakkun bayanai kan manyan sassan uku na shirin AGILE, tattaunawa tsakanin mahalarta, da zaman tambayoyi da amsoshi inda malamai suka gabatar da tambayoyi kan wasu bangarorin shirin kuma aka basu bayanai dalla-dalla.

Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai39 minutes ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai20 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara