Labarai
Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin arziki da al’adun ƙasar nan.
Tsohon Daraktan gudanarwa na Radio Nigeria Kaduna kuma gogaggen ɗan jarida, Alhaji Halilu Ahmad Getso, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da wakilin Radio Nigeria a Kano, a wani ɓangare na bikin cika shekaru 75 da kafuwar gidan rediyon.
Getso ya ce asalin kafuwar wannan hukuma ya samo tushe ne tun zamanin Nigerian Broadcasting Corporation (NBC), wadda aka kafa a lokacin marigayi Firimiya na Arewacin Najeriya, Ahmadu Bello.
Ya bayyana cewa a farkon shekarun, an kafa ƙananan tashoshi ne kawai a Kano da Maiduguri, waɗanda ake haɗawa da Kaduna domin watsa shirye-shirye da kuma daidaita ayyukan rediyo.
A cewarsa, gidan rediyon ya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa rayuwar al’umma ta hanyar shirye-shirye masu tasiri da suka mayar da hankali kan bukatun jama’a, ilimi da kuma kyawawan ɗabi’u.
Gogaggen ɗan jaridar ya kuma tuna da yadda hukumomin tsohuwar gwamnatin yankin Arewa suka sayo rediyo tare da rarraba su ga al’ummomin karkara domin ƙara musu damar samun bayanai da sadarwa.
Ya ƙara da cewa a wancan lokaci, shahararrun shirye-shirye sun haɗa da karatun Alƙur’ani da kuma shirye-shiryen da suka shafi ci gaban al’umma, waɗanda suka ja hankalin masu sauraro da dama.
Getso ya kuma bayyana cewa yawancin ma’aikatan Hukumar Rediyon Tarayya ta Najeriya (FRCN) a yanzu, sun fara aiki ne tun a NBC, abin da ke nuna ci gaba da gogewa a cikin tsarin aikin.
Ya ce kamfanin watsa shirye-shirye na Arewacin Najeriya, wanda shi ma aka kafa a ƙarƙashin jagorancin Ahmadu Bello, daga bisani ya rikide zuwa Radio Nigeria Kaduna, lamarin da ya ƙarfafa harkar watsa shirye-shirye a yankin.
Yayin da yake yaba gudunmawar da gidan rediyon ya bayar tsawon shekaru, Getso ya buƙaci ma’aikata su ƙara ƙaimi wajen inganta ayyukan su domin su dace da sabbin ƙa’idojin aikin watsa shirye-shirye na zamani.
Haka kuma, ya yi addu’ar fatan alheri ga ci gaba da ɗaukakar Radio Nigeria da sauran tashoshin FRCN a faɗin ƙasar.
Abdullahi Jalaluddeen, Kano
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
-
Labarai7 days agoHukumar Lafiya a Kano ta Shirya Taron Masu Ruwa da Tsaki Kan Cutar Shan Inna
