Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Borno Za Ta Kashe Naira Biliyan Daya Don Horar Da Malaman Makarantu

Published

on

Gwamnatin Jihar Borno ta amince da kashe naira miliyan dubu daya domin horar da malaman makarantun firamare a fadin kananan hukumomi ashirin da bakwai na jihar.

Gwamna Babagana Zulum ya amince da hakan ne a lokacin da yake kaddamar da sabbin sakatarorin ilimi na kananan hukumomi da aka nada a Maiduguri.

Ya yi nuni da cewa sama da malamai dubu daya da ke da takardar shaidar kammala karatun sakandare za su kara samun horon da zai ba su damar samun karancin cancantar koyarwa.

Horon zai hada da malaman da ba su da kwarewar koyarwa amma an gano cewa za su iya ba da horo bisa bayanan gwajin cancantar da aka yi musu,” in ji Zulum.

Gwamnan ya bukaci sabbin sakatarorin ilimi da aka nada da su maida hankali akan aikinsu, inda ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu da gazawa za a maye gurbinsa.

Na umurci mai girma kwamishinan ilimi da ya ba ni rahoto kan ayyukan kowace sakatariyar ilimi. Za a maye gurbin wadanda suka kasa cimma bukatun gwamnati,” in ji Zulum.

Kwamishinan ilimi, kimiya, fasaha da kirkire-kirkire, Lawan Wakilbe, ya ce mutane 126 ne suka nemi wannan matsayi kuma bayan kammala jarrabawar tantancewa, an zabo ashirin da bakwai bisa ga kwazon da suka yi.

A halin da ake ciki, Gwamna Babagana Zulum ya bayar da motocin  hamsin da takwas ga sakatarorin ilimin  da jami’an sa ido a fadin kananan hukumomi ashirin da bakwai da ke jihar.

 

Dauda Iliya

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai4 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara