Ilimi
Gwamnatin Borno Za Ta Kashe Naira Biliyan Daya Don Horar Da Malaman Makarantu
Gwamnatin Jihar Borno ta amince da kashe naira miliyan dubu daya domin horar da malaman makarantun firamare a fadin kananan hukumomi ashirin da bakwai na jihar.
Gwamna Babagana Zulum ya amince da hakan ne a lokacin da yake kaddamar da sabbin sakatarorin ilimi na kananan hukumomi da aka nada a Maiduguri.
Ya yi nuni da cewa sama da malamai dubu daya da ke da takardar shaidar kammala karatun sakandare za su kara samun horon da zai ba su damar samun karancin cancantar koyarwa.
” Horon zai hada da malaman da ba su da kwarewar koyarwa amma an gano cewa za su iya ba da horo bisa bayanan gwajin cancantar da aka yi musu,” in ji Zulum.
Gwamnan ya bukaci sabbin sakatarorin ilimi da aka nada da su maida hankali akan aikinsu, inda ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu da gazawa za a maye gurbinsa.
“Na umurci mai girma kwamishinan ilimi da ya ba ni rahoto kan ayyukan kowace sakatariyar ilimi. Za a maye gurbin wadanda suka kasa cimma bukatun gwamnati,” in ji Zulum.
Kwamishinan ilimi, kimiya, fasaha da kirkire-kirkire, Lawan Wakilbe, ya ce mutane 126 ne suka nemi wannan matsayi kuma bayan kammala jarrabawar tantancewa, an zabo ashirin da bakwai bisa ga kwazon da suka yi.
A halin da ake ciki, Gwamna Babagana Zulum ya bayar da motocin hamsin da takwas ga sakatarorin ilimin da jami’an sa ido a fadin kananan hukumomi ashirin da bakwai da ke jihar.
Dauda Iliya
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar