Labarai
Kaduna: Gwamna Uba Sani Ya Tsabtace Harkokin Hajji – NUJ
An yabawa Gwamna Uba Sani saboda tsabtace harkokin hajji da kuma naɗa kwararru don jagorantar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna.
Shugaban Kungiyar Yan Jaridu ta Kasa reshen Jihar Kaduna, Alhaji AbdulGafaar Alabelewe, ne yayi yabo yayin da jami’an kungiyar suka kai ziyarar ban girma ga hukumar.
NUJ ta kuma bayyana naɗin Malam Salihu S. Abubakar a matsayin Shugaban Hukumar a matsayin wanda ya dace da mukami, inda suka jaddada cewa gaskiyarsa da bin doka da na da matukar muhimmanci wajen ci gaban hukumar.
Alhaji AbdulGafaar ya ce hukumar ta samu nasarori masu yawa a lokacin hajjin da ya gabata, ciki har da maidawa kowane mahajjaci dala 50 daga kudin hadaya da suka biya a Najeriya.
Ya kuma ce mahajjatan jihar Kaduna sun sami matsuguni kusa da Masallacin Harami a Makka, kuma farashinsa ya kasance kasa da wanda Hukumar Kula da Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tsara.
A cewarsa, maidawa mahajjatan shekarar 2023 naira 61,080 cikin gaggawa ya nuna cewa Malam Salihu da kwamitinsa suna da kwazo da himma wajen gyara harkokin hajji.
Alabelewe ya kuma yaba da gyaran da hukumar ta yi wa sansanin mahajjata na Mando, yana mai danganta nasarorin da gaskiya da rikon amana na shugabancin hukumar.
Shugaban NUJ ya sha alwashin ci gaba da hada hannu da hukumar wajen wayar da kan maniyyata, tare da kira ga ‘yan jaridu da su bai wa hukumar cikakken hadin kai.
Da yake mayar da martani, Malam Salihu ya gode wa ‘yan jaridu bisa kyakkyawar dangantaka da hukumar, tare da alkawarin ƙarfafa hulda da su. Ya bukaci su dinga tantance labarai masu shakku kafin wallafawa, yana mai cewa, “kofarmu a bude take don karin bayani.”
Shugaban hukumar ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa goyon bayansa, yana mai cewa duk nasarorin da aka samu saboda tallafinsa ne.
Rel/Adamu Yusuf
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai19 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
