Connect with us

Labarai

NLC jihar Plateau ta bi sahun takwarorinta wajen zanga zangar tsadar rayuwa.

Published

on

Shugaban kunguyar a Jihar Plateau Comrade Eugene Manji yace tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasan Nan ya wuce tunanin kowane Dan kasan Nan.

Masu gangamin sunyi kwanba a shataletalen sakatariyar jihar inda suka bayyana irin damuwar da suke cikinta game da wannan tsaadar rayuwa da ta musu dabaibayi.

Shuganan kungiyar a jihar Plateau Comrade Eugene Manji yace cire tallafin Mai ba tare da wani kwakkwaran shiri ba, shi ne ummul’aba’isin fadawa cikin wannan masifar.

Hakama ya bayyana matukar damuwarsu game da canjin kudaden kasashen waje ya kasance.

Comrade Manjin duk da haka Kuma, gwamnati ta kasa cika alkawarinta na samarda motocin safa safa masu amfani da gas da gyaran matatun man fetur, da wutar lantarki da dai sauran matakan rage tsadar rayuwar ga ‘yan Nijeriya.

Ya bayyana matukar damuwarsa ganin cewa duk da tashin gwaron zabin kusan komai a kasan nan, amma albashin da ake biyan ma’aikata bai taka kara ya karya ba.

Sannan ya godewa ‘yan kwadago saboda amsa Kiran da sukayi suka yi fitowar farin dango duk irin matsin rayuwar da ake ciki, tare da shan alwashin kungiyar kwadago zata ci gaba da Kare hakkin ma’aikata da ‘yan Nijeriya ba tare da gajiyawa ba.

Farfesa Kiri Jaryam shi ne yayi magana a madadin kungiyar malaman jami’a ya bukaci dukkannin ‘yan Nijeriya da su hada kansu don a gudu tare a tsira tare.

Dr. Makuyai Godwin yayi magana a madadin kungiyar malaman kwalejojin kimiyya da fasaha da kuma Anthony Joro da ya wakilci kungiyar manyan ma’aikata sun bukaci gwamnati ta tabbatar da ‘yan Nijeriya sun sami saukin rayuwa.

Josiah/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai6 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara