Connect with us

Labarai

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Published

on

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin Kwararru ta Murtala Muhammad dake Kano, yayin da sauran huɗun ke ci gaba da samun kulawa ta musamman.

A cikin wata sanarwa da jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar, Samira Suleiman ta fitar, ta ce an haifi jariran ne kafin cikar wa’adin haihuwa, inda aka kwantar da su a sashen kula da jarirai masu buƙatar kulawa ta musamman, domin jinyar matsalolin ƙarancin nauyi da haihuwa da wuri  da sauran matsaloli masu alaƙa da hakan.

Hukumar ta bayyana cewa nan take aka sanya dukkan jariran biyar a karkashin kulawa ta musamman, ciki har da amfani da na’urar incubator, da kuma magungunan rigakafin cututtuka, waɗanda daga bisani aka ƙara inganta su bisa ga yadda yanayin lafiyarsu ke buƙata.

Da take bayani kan halin da suke ciki, hukumar ta ce jariri na farko, mace mai nauyin kilo 1.3, ta rasu duk da an yi mata ƙarin jini, sakamakon matsalolin da suka shafi tsayawar numfashi (apnoea).

A cewar hukumar, dukkan jariran sun fuskanci matsalar saukar sukarin jini (hypoglycaemia), amma an shawo kan lamarin cikin gaggawa bisa ƙa’idojin likitanci.

Haka kuma, ta ce ana yi wa dukkan jariran hasken jinya (phototherapy) domin magance ciwon jaundice na jarirai, wanda galibi ke faruwa ga waɗanda aka haifa da wuri.

Ƙarƙashin jagorancin shugaban hukumar, Mansur Mudi Nagoda, HMB ta ce an ɗauki dukkan matakan jinya da suka dace tun daga lokacin haihuwa har zuwa kulawar da ake ci gaba da yi musu.

Duk da haka, hukumar ta jaddada cewa irin waɗannan haihuwar jarirai da yawa a lokaci guda kafin lokaci na da matuƙar haɗari a fannin likitanci, duk da ƙoƙarin da ake yi na ba su kulawa mafi inganci.

Hukumar ta kuma yaba da ƙwazon da jajircewar ma’aikatan lafiya na sashen haihuwa da na kula da jarirai, tana mai cewa matakan gaggawa da suka ɗauka na taka muhimmiyar rawa wajen kula da jariran da suka rage.

Khadijah Aliyu

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara