Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamnatin Jihar Jigawa ta kara jaddada kudirinta na ci gaba da ilimantarwa tare da wayar da kan maniyyata aikin Hajjin bana.

Darekta Janar na Hukumar Jin dadin Alhazan Jihar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Yana mai cewar ilimantarwa tare da wayar da kan maniyyatan jihar na daya daga cikin abubuwan da hukumar ta sanya a gaba domin samun nasarar da ta dace.

Ya kara da cewar, hukumar tana da malaman bita da za su taimaka wa maniyyatan wajen sauke farali a kasar Saudiyya.

A don haka, Labbo ya bukaci maniyyatan da su maida hankali wajen halartar wuraren bita a kananan hukumomin su.

Ya yi nuni da cewar, halartar taron bitar zai kara musu ilimin sanin yadda za su gudanar da aikin hajji karbabbe gami da
baiwa maniyyatan damar samun sakonni dake fitowa daga hukumar dangane da shirye-shiryen da suka shafi aikin Hajji.

Darekta Janar din ya bayyana cewar, tuni hukumar ta fara tantance lafiyar maniyyatan a ci gaba da shirye-shiryen da take yi.

Ya yabawa Gwamna Umar Namadi da sauran masu ruwa da tsaki bisa gudunmawar da suke baiwa hukumar a kowane lokaci domin cimma burin da aka sanya a gaba.

 

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara