Connect with us

Labarai

An Kaddamar da Yin Allurar Rigakafi ga Maniyyatan Jihar Jigawa

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ƙaddamar da aikin yi wa Maniyyata aikin Hajjin 2026 allurar rigakafi.

Babban Daraktan Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse.

A cewarsa, wannan aiki na daga cikin shirye-shiryen da ake ci gaba da yi domin gudanar da aikin Hajjin 2026, inda ya jaddada kudirin hukumar na bai wa lafiyar Alhazan jihar muhimmanci.

Ya ce, kare lafiyar Alhazan jihar wajibi ne kuma nauyi ne da ya rataya a wuyan hukumar.

Wannan aikin allurar rigakafi yana nuna shirye-shiryenmu na ganin an gudanar da Hajjin 2026 cikin nasara. Ina kira ga dukkan Alhazai da su bayar da cikakken hadin kai tare da bin ka’idojin lafiya yayin da suke shirin wannan tafiya mai alfarma.”

“Ina kuma karfafa muku gwiwa da ku kasance masu bin doka da oda tare da yin hakuri a duk tsawon lokacin aikin Hajji. Ku tabbata kun halarci dukkan tarukan wayar da kai, domin za ku sami muhimman bayanai kan yadda ake gudanar da ibadar Hajji da kuma shawarwari masu amfani ga tafiyar da ke gabanku,” In ji Labbo.

Labbo, wanda ya zagaya wajen aikin allurar rigakafin, ya ce za a ci gaba da gudanar da aikin har zuwa lokacin tashi zuwa kasa mai tsarki.

A nasa jawabin, Daraktan Ayyuka na Hukumar, Alhaji Muhammad Garba, ya sake jaddada muhimmancin bin dukkan dokoki da ka’idojin da hukumomin ƙasar Saudiyya suka shimfida domin cimma burin da ake so.

Shi ma da yake jawabi, Shugaban Tawagar Lafiya, Dakta Abubakar Habib, ya bayyana cewa an samar da isassun alluran rigakafi, da za a yi wa dukkan Maniyyatan.

Ya bayyana muhimmancin alluran da ake yi, wadanda suka hada da na sankarau, da na shan inna, da kuma zazzabin shawara.

Wadannan allurai wajibi ne bisa dokokin lafiya na Masarautar Saudiyya. Allurar zazzabin shawara tana aiki na tsawon shekaru goma, yayin da ta sankarau ke aiki na tsawon shekaru uku. Suna da matukar muhimmanci wajen kare lafiyar mutum da ta al’umma baki daya,” in ji Dakta Habib.

Wakilinmu ya ruwaito cewa ana gudanar da aikin allurar rigakafin a dukkan kananan hukumomi 27 na jihar.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara