Kasuwanci
An Fasa Rumbun Abincin Gwamnati A Jihar Kebbi
Wasu mutane sun fasa rumbun abincin gwamnati a Jihar Kebbi da ke Unguwar Bayan Kara a Birnin Kebbi a ranar Lahadi.
Mutanen da suka fasa rumbun sun yi galaba ne a kan jami’an tsaron da ke tsare da rumbun na gwamnati.
An bayyana cewa bayan Rumbun Gwamnati da aka fasa, mutanen sun wawushe kayan abincin da ke makare a wata mota da ta lalace a kan hanya.
Shugaban ’yan kasuwar Bayan Kara dake Birnin Kebbi Muhammadu Gwadangwaji ya ce, ba Rumbun Gwamnati kadai mutane suka fasa ba.
A cewarsa, an fasa wasu shagunan ’yan kasuwa an kuma cinna wa wasu wuta, duk da irin ƙoƙarin da jami’an tsaro suka yi.
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris; Ahmed Idris, ya bayyana lamarin a matsayin “abin takaici”.
Ya bayyana cewa: “Tun da farko an samu wasu ɓata-gari sun kai hari kan kayan abinci da Dangote ya aiko jiharmu domin rabawa jama’a sannan suka garzaya ma’ajiyar gwamnati inda nan ma suka kwashe wasu kayan abincin.
“Irin wannan lamari bai taba faruwa a Kebbi ba. Kayayyakin abincin da suka wawashe na daga cikin kayan abincin da gwamnatin jihar ta siya domin raba wa al’umma“.
Ya ce, gwamnati ta ɗauki matakin kare ma’ajiyar ta domin hana afkuwar irin haka anan gaba.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato