Connect with us

Labarai

Tinubu Ya Nemi Shugabannin Addini Su Daina La’antar Kasan Nan A Wa’azinsu

Published

on

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi kira ga malamai da shugabannin addini da su guji “ƙasƙantarwa da kuma la’antar ƙasar” a cikin wa’azi kuma huɗubobinsu.

 

Tinubu ya yi kiran ne ranar Alhamis yayin da yake buɗe-baki tare da sarakuna da kuma jagororin addinin Musulunci da na Kirista a fadar shugaban ƙasa, yana mai jaddada cewa wa’azin da suke yi yana da matuƙar tasiri a cigaban ƙasar.

 

“Kishin ƙasar nan yana hannunku. Ku yi mata addu’a, ku ilimantar da yaranmu. Huɗubar da muke yi a masallatai da coci-coci na da matuƙar muhimmanci,” in ji shi.

 

Ya ƙara da cewa: “Kada ku la’anci ƙasarku…Idan shugaba ba mutumin kirki ba ne ku bari zaɓe ya zo ku sauya shi, amma kada ku la’anci ƙasar. Da ma an tsara shugabanci ne da nufin kawo sauyi.”

 

Sarkin Zazzau Nuhu Bamalli ne ya wakilci Mai Alfarma Sarkin Musulmi Abubakar Sa’ad III a taron, wanda ya samu halartar Sakataren Ƙungiyar Kiristoci ta CAN Samson Fatokun.

Shi ma Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya nemi malaman da su “dinga haɗa kan al’umma don guje wa rikicin ƙabilanci da na addini”.

Labarai

Labarai8 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara