Labarai
Kungiyar Marayu Ta Yi Kira Ga Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gina Wa Mata Cibiyar Koyan Sana’o’i.
Kungiyar Marayu ta Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna ta taimaka mata wajen gina cibiyar koyarda sana’o’i.
Shugabar kungiyar, Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta yi wannan kiran a wurin taron rabawa Marayu Kayayyaki da ya gudana a harabar ofishin kungiyar dake Barnawa Kaduna
Ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen samarwa mata da matasa hanyar sana’o’i domin su dogara da kansu.
Har ila yau, ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen kawarda ayyukan shaye-shaye a tsakanin matasa da kuma rage radadin talauci a tsakanin al’umar yankin.
Da take tsokaci a wurin taron, shugabar kungiyar Nisa’us Sunnah dake Barnawa Kaduna, Malama Amina Namadi tace Kungiyar Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta kwashe shekaru 14 wajen ayyukan kulada marayu ta hanyar tara taro-sisi a tsakanin mambobinta.
Ta kara da cewa, a haka kungiyar ta dauki alhakin kulada marayu 10 tun suna kanana har suka kai wani mataki ta hanyar sanyasu a makaranta da ciyarda su da tufatarda su tareda koya musu sana’o’in hannu.
Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin Hauwa Usman da Usman Bala, sun godewa Kungiyar bisa wannan yunkuri, tareda addu’ar samun daukaka don kaiwa ga babban matsayi.
Kayayyakin da kungiyar ta raba su ne, kayan abinci da masarufi ga marayunta 12, sai kuma kayan Sallah ga sauran marayu maza da mata 60.
Khadija Kubau
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United