Connect with us

Labarai

Kungiyar Marayu Ta Yi Kira Ga Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gina Wa Mata Cibiyar Koyan Sana’o’i.

Published

on

 

Kungiyar Marayu ta Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna ta taimaka mata wajen gina cibiyar koyarda sana’o’i.

Shugabar kungiyar, Malama Rabi’atu Adam Isma’il ta yi wannan kiran a wurin taron rabawa Marayu Kayayyaki da ya gudana a harabar ofishin kungiyar dake Barnawa Kaduna

Ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen samarwa mata da matasa hanyar sana’o’i domin su dogara da kansu.

Har ila yau, ta ce samarda cibiyar zai taimaka wajen kawarda ayyukan shaye-shaye a tsakanin matasa da kuma rage radadin talauci a tsakanin al’umar yankin.

Da take tsokaci a wurin taron, shugabar kungiyar Nisa’us Sunnah dake Barnawa Kaduna, Malama Amina Namadi tace Kungiyar Jam’iyyatu Tukaful Aytam ta kwashe shekaru 14 wajen ayyukan kulada marayu ta hanyar tara taro-sisi a tsakanin mambobinta.

Ta kara da cewa, a haka kungiyar ta dauki alhakin kulada marayu 10 tun suna kanana har suka kai wani mataki ta hanyar sanyasu a makaranta da ciyarda su da tufatarda su tareda koya musu sana’o’in hannu.

Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin Hauwa Usman da Usman Bala, sun godewa Kungiyar bisa wannan yunkuri, tareda addu’ar samun daukaka don kaiwa ga babban matsayi.

Kayayyakin da kungiyar ta raba su ne, kayan abinci da masarufi ga marayunta 12, sai kuma kayan Sallah ga sauran marayu maza da mata 60.

Khadija Kubau

Labarai

Labarai6 mins ago

HARIN MASALLACIN KANO: Obi Ya Ziyarci Wadanda suka Mutu

  Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya ziyarci wadanda kona masallacin Kano...

Labarai25 mins ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Ta Yi Kiran A Yiwa Mijinta Addu’a

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce addu’a ita ce ginshikin duk wani shugabanci mai nasara, don...

Labarai43 mins ago

Gwamnatin Kano Ta Rufe Asibitin Kwanar Ganduje A Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta rufe tare asibitin Kwanar Ganduje dake unguwar Sharada Karamar Hukumar Kano Municipal.   Babban daraktan hukumar...

Labarai1 hour ago

Shugaban Iran Ebrahim Raisi Ya Rasu A Hatsarin Jirgi

Jami’an Iran sun ce Shugaba Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar, Hossein Amir-Abdollahian sun rasu a wani hatsarin jirgin...

Labarai12 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Mafi Shahara