Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Bukaci’Yan Majalisa Su Tsagaita Gayyatar Shugabannin Ma’aikatu

Published

on

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya roƙi ’yan Majalisar Wakilai da su daina yawan yi wa ministoci da shugabannin hukumomin Gwamnatin Tarayya kiranye da titsiye su kan ayyukan da suke gudanarwa.

Tinubu ya yi wannan roƙo ne yayin jawabinsa a wurin buda bakin da aka shirya wa ’yan Majalisar Wakilan ranar Laraba a Abuja.

Shugaban ya ce duk da cewa sa ido yana da matukar muhimmanci wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana a harkokin mulki, gayyato jami’ai fiye da kima na iya firgitasu ya kuma kawo cikas a tasirin ayyukan da za a yi wa ‘yan Najeriya.

Ya bukaci ‘yan majalisar da su nuna kwarewa wurin gudanar da ayyukansu na sa ido.

“Ina ganin yadda kwamitoci daban-daban su ke kiran ministoci da shugabannin hukumomi. Na kai kuka ga Shugaban Majalisa da cewa a bar talaka ya sarara.

“A bari mutanen nan su yi aikinsu. Ba ina cewa ba ku da tasiri ba ne, ba kuma ina cewa ku daina sa ido akan ayyukan da ake yi a ma’aikatu ba ne, roƙon da nake yi shi ne, ku barsu su yi aiki.

“Amma ku yi la’akari da aikin da kowace hukuma da ma’aikatanta ke yi. Kamar ayyukan da ke kan Gwamnan Babban Bankin ko kuma Ministan Tattalin Arziki na Kasa da Kudi da sauran al’umma baki ɗaya.

“Idan hankalinsu ya zama ba a kwance ba ko kuma suna kidime, to abubuwan ba za su tafi yadda kowa ke so ba, watakila sai kun fara zaman majalisa har cikin dare.

“Dole ne mu nemo hanyar da za mu zaunar da juna. Wannan roƙo ne gare ku. Ku duba yiwuwar amincewa da wakilan shugabannin ma’aikatu da ministoci a wasu lokuta ko ma takardu.”

Shugaba Tinubu ya bayyana jin dadinsa dangane da yadda Majalisar Dokokin ke ayyukanta.

Ya kuma jaddada godiya da jin daɗinsa akan yadda ake samun jituwa tsakanin bangaren zartarwa da Majlisar dokoki.

Ya ce, kyakkyawar alaƙar da ke tsakani ta ba majalisar damar amincewa da kudurorin bangaren zartarwa da a yanzu ‘yan Najeriya ke mora.

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara