Labarai
NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kebbi ta raba kayan abinci da kudi ga iyalan mambobinta da suka rasu a lokacin da suke kan aikin jarida, a matsayin kyautar azumin Ramadan.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kungiyar na Jiha, Kwamared Bello Sarki Abubakar, ya ce suna gudanar da wannan shiri a duk shekara, tun bayan kaddamar da shi da tsohon shugaban kungiyar na jiha Alhaji Aliyu Jajirma ya yi, domin faranta ran iyalan abokan aikinsu da suka rasu.

Kwamared Sarki Abubakar ya bayyana cewa dukkan shugabannin kungiyar da suka gabata sun tabbatar da ci gaba da gudanar da wannan shiri a duk lokacin azumin Ramadan domin rage wa iyalan mamatan radadin wahalhalun rayu.
Ya sanar da cewa kowane iyali daga cikin iyalan mambobi 21 da suka rasu za su karɓi buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 25 da kuma naira dubu goma.

Yayin da yake gode wa Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin jagorancin Kwamared Nasiru Idris saboda goyon bayan da take bai wa kungiyar, Kwamared Sarki ya yaba da ayyukan ci gaba da Gwamna Nasir Idris ya aiwatar a cikin shekaru biyu da suka gabata domin inganta rayuwar al’ummar jihar.
Kwamishinan Watsa Labarai da Al’adu na Jihar Kebbi, Alhaji Yakubu Ahmed BK, yayin da yake yaba wa shugabancin kungiyar saboda tallafin da ta bai wa iyalan mamatan, ya tabbatar wa kungiyar cewa Gwamnatin jihar za ta ci gaba da fifita jin daɗin ‘yan jarida a jihar.

Haka kuma, ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa badi an gudanar da wannan taro cikin gagarumin shiri domin faranta wa iyalan mamatan rai.
A madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daya daga cikin matan wadanda suka rasu, Hajiya Hadiza Abdullahi, ta gode wa kungiyar saboda tunawa da su bayan rasuwar mazajensu.
Daga Abdullahi Tukur
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
