Connect with us

Ilimi

Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Dauki Nauyin Dalibai 80 Da Ke Manyan Makarantu

Published

on

Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa ta ce za ta dauki nauyin dalibai ‘yan asalin yankin su 80 da ke kwalejin Ilmi ta tarayya ta Jama’are a Jihar Bauchi, da kwalejin fasaha ta Dutse da kuma kwalejin fasahar sadarwa ta Kazaure.

Shugaban Karamar Hukumar, Dr. Muhammed Uba Builder ya bayyana haka ga manema labarai a Birnin Kudu.

Dr Muhammad Uba, yayi bayanin cewar, an zabo mutum uku-uku daga kowace mazaba goma sha daya dake yankin.

Yana mai cewar, Karamar Hukumar ta yanke shawarar hakan ne domin bai wa dalibai damar karatu cikin sukuni.

Dr Muhammad Uba Builder, ya kara da cewar nan gaba kadan Karamar Hukumar za ta kara zabo wasu daliban dan tafiya manyan jami’o’i dake kasar nan.

A cewarsa, an kafa kwamati dan tantancewa daliban da suka cancanta.

A nasa jawabin Shugaban kwamatin tantance daliban kuma shugaban ma’aikata na yankin Yarima Musa, ya ce za su zabo daliban da suka cancata domin tura su makarantun da suka dace.

Ya kuma ya yabawa Shugaban Karamar Hukumar ta Birnin Kudu bisa namijin kokarinsa wajen daukar nauyin karatun daliban domin samun ingantacciyar rayuwa mai amfani a nan gaba.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai18 hours ago

Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran

Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar. Masu...

Labarai18 hours ago

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga...

Kasuwanci18 hours ago

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a...

Kasuwanci18 hours ago

Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukaci Kiristoci da su yi tunani a kan darussa, muhimmaci, da kuma kyawawan dabi’u...

Kasuwanci18 hours ago

Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.

Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma...

Kasuwanci18 hours ago

Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa za ta gudanar da atisayen harbe-harbe ga sabbin ‘yan sanda a karamar...

Labarai19 hours ago

Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka

    Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman...

Labarai1 day ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

  Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare...

Fasaha2 days ago

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye...

Kasuwanci2 days ago

Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da...

Mafi Shahara