Connect with us

Labarai

Jigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Tawagar Hukumar jin dadin Alhazai ta Jihar jigawa ta kai ziyarar taya murna ga Amirul Hajji na bana kuma Mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji Hamim Nuhu Muhammadu Sanusi.

Jagoran tawagar kuma Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bada tabbacin baiwa Amirul Hajjin cikakken hadin kai da goyan baya domin samun nasarar jagorantar aikin hajjin bana.

 

Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya kuma yiwa Mai Martaba Sarki bayanai game da inda aka kwana game da shirye-shiryen aiki Hajjin bana wanda ya tasamma kaso 40 cikin 100.

Kazalika, ya kuma yi wa Mai martaban bayani akan nasarorin da hukumar ta samu kan batun karbar lamuni daga gwamnatin Jihar domin tare kujerun aikin Hajjin bana.

Ya kuma jaddada cikakken hadin kai da goyan bayansa da na ma’aikatan hukumar ga Amirul Hajji domin sauke nauyi da aka dora masa na jagorantar Alhazan 2026.

A jawabinsa, Mai Martaba Sarkin kuma Amirul hajjin, ya bayyana jin dadin sa da wannan ziyara.

Ya kuma yabawa hukumar kan tsare tsarenta game da aikin hajjin bana.

Ya na mai nuni da cewar, a matsayinsa na jagora, zai yi aiki tare da hukumar domin samun nasarar gabatar da aikin hajjin bana.

A cewar sa, kamar yadda aka samu nasarar aikin hajjin a 2025,a bana ma za’a samu fiye da bara da izinin Allah.

 

 

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara