Labarai
BIKIN KARAMAR SALLAH: NSCDC Ta Tura Jami’ai 3,200 a Kano.
Rundunar tsaron farin kaya ta Najeriya, reshen jihar Kano, ta kammala dukkan shirye-shiryen tsaro da suka dace domin gudanar da bukukuwan karamar Sallah lafiya a jihar.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SC Ibrahim Idris Abdullahi ya fitar, ya ce kwamandan jihar, Mohammed Lawal Falala, ya amince da tura jami’ai sama da dubu uku da dari biyu a fadin jihar.
Jami’an da aka zabo daga ofisoshi na yanki da ma’aikatun za suyi aiki a filayen Idi daban-daban, wuraren shakatawa da ke a fadin Kano.
Sanarwar ta tabbatar da an tsara tsaro tare da dakile yiwuwar karya doka da oda kafin bukukuwan Sallah da bayan bukukuwan Sallah.
Sannan hukumar ta gargadin ‘yan daba da bata gari da su nisanta kansu daga duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiyar al’umma.
Jami’an rundunar a kodayaushe suna nan a kasa kuma a shirye suke don murkushe duk wanda aka kama yana karya doka a jihar.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana