Connect with us

Kasuwanci

Gwamnati Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000 A Sakkwato

Published

on

Gwamnatin Tarayya, ta ƙaddamar da rabon tan 42,000 na hatsi ga mabuƙata a Jihar Sakkwato.

Rabon wani ɓangare ne na umarnin shugaba Bola Tinubu, na tallafa wa marasa ƙarfi da abinci a halin matsin rayuwa da ake fuskanta a Najeriya.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne, ya bayyana hakan ranar Lahadi a shafinsa na X (Twitter).

Ya ce “Na bi sahun gwamnan Sakkwato, Ahmed Aliyu da abokan aikina, ministan noma da samar da abinci da ƙaramin minista Sabi Aliyu wajen ƙaddamar da rabon.”

Hukumar Bayar da Agaji ta Kasa (NEMA), za ta sanya ido kan rabon tare da taimakon hukumomin tsaro domin tabbatar da gaskiya da adalci.

A cewar ministan, kowace jiha a faɗin Najeriya za ta ci gajiyar rabon “Za mu tabbatar mun bayar da ƙarin bayani kan shirin.”

Tun farkon watan Maris ne, Shugaba Bola Tinubu, ya bayar da umarnin fara raba hatsin a faɗin jihohin Najeriya 36 da ke ƙasar nan.

Wannan dai na zuwa ne bayan cire tallafin man fetur da Shugaba Tinubu ya yi wata 10, bayan karɓar mulki a watan Mayun 2023.

Cire tallafin ya janyo hauhawar farashin kayayyakin masarufi, lamarin da ya kai ga gudanar da zanga-zanga a wasu jihohin ƙasar nan.

NASIR MALAMI/Wababe

Labarai

Labarai15 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai16 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai17 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi18 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara